49 lines
2.2 KiB
Markdown
49 lines
2.2 KiB
Markdown
# Allah
|
|
|
|
## Ma'ana
|
|
|
|
A cikin Littafi Mai Tsarki, kalmar nan "Allah" tana nufin rayayyen nan da ya hallici komai ba daga cikin komai ba. Allah yana nan a matsayin Uba, Ɗa, da Ruhu Mai Tsarki. Ainahin sunan Allah shi ne "Yahweh."
|
|
|
|
* Allah na nan a kullum; ya kasance kafin komai ya kasance kuma zai ci gaba da kasancewa har abada.
|
|
* Shi ne kaɗai Allah na gaskiya yana kuma da iko akan komai da ke cikin duniya.
|
|
* Allah cike yake da adalci, mai matuƙar hikima, mai tsarki, marar zunubi, adali, mai jinƙai, da kuma ƙauna.
|
|
* Shi Allah ne mai riƙe alƙawari, wanda ke cika alƙawarinsa a kullum.
|
|
* An hallici mutane nedomin su bautawa Allah kuma shi kaɗai za su bautawa.
|
|
* Allah ya baiyana sunansa da "Yahweh" wanda ke nuna "shi ne" ko "ni ne" ko "Wanda har kullum yana nan."
|
|
* Hakanan Littafi Mai Tsarki yana koyar da mu game da "allolin" ƙarya waɗanda gumaka ne mara sa rai rai da mutane ke bautawa cikin kuskure.
|
|
|
|
|
|
Shawarwarin Fassara:
|
|
|
|
* Hanyoyin da za'a fassara "Allah" za haɗa da "Mahallici" ko "Siffa" ko Mai Iko."
|
|
* Waɗansu hanyoyin da za'a yi fassarar "Allah" su ne "Mahallici Mai Iko Dukka" ko "Ubangijin Dukkan Hallita" ko "Madawwamin Mahallici."
|
|
* Yi la'akari da yadda ake kiran Allah a naku harshen da ake fassara. Idan haka ne yana da muhimmanci a tabbatar cewa wanan kalma ta yi daidai da ɗabi'ar Allah na gaskiya da aka ambata a sama.
|
|
* Harsuna da yawa kan mori babban baƙi na farko a rubuta suna Allah na gaskiya domin bambanta shi da allahn ƙarya.
|
|
* Wata hanya kuma da zata sa wanan ya zama ikakke ita ce moron wata kalmar domin ambaton "Allah" da kuma "gunki."
|
|
* Kalmar nan "zan zama Allahnsu za su zama mutanena" za'a iya fassara ta da "Ni Allah zan yi mulki bisa waɗanan mutane za su kuma yi mini sujada."
|
|
|
|
|
|
(Hakanan duba: hallita, allahn ƙarya, Allah Uba, Ruhu Mai Tsarki, allahn ƙarya, Ɗan Allah, Yahweh)
|
|
|
|
|
|
Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:
|
|
|
|
* Yahaya 01:7
|
|
* 1 Sama'ila 10:7-8
|
|
* 1 Timoti 04:10
|
|
* Kolosiyawa 01:16
|
|
* Maimaitawar Shari'a 29:14-16
|
|
* Ezra 03:1-2
|
|
* Farawa 01:2
|
|
* Hosiya 04:11-12
|
|
* Ishaya 36:6-7
|
|
* Yakubu 02:20
|
|
* Irmiya 05:5
|
|
* Yahaya 01:3
|
|
* Yoshuwa 03:9-11
|
|
* Littafin Makoki 03:43
|
|
* Mika 04:5
|
|
* Filibiyawa 02:6
|
|
* Littafin Misalai 24:12
|
|
* Zabura 047:9
|