ha_tw/bible/names/cain.md

743 B

Kayinu

Gaskiya

Kayinu da ƙanensa Habila sune 'ya'ya maza na Adamu da Hauwa'u da aka faɗi a Litttafi Mai Tsarki.

  • Kayinu manomi ne wanda ya noma kayan abinci Habila kuwa makiyayin tumaki ne.
  • Kayinu ya kashe ɗan'uwansa Habila a cikin hasalar ƙyashi, saboda Allah ya karɓi hadayar Habila, amma bai karɓi hadayar Kayinu ba.
  • Horon da Allah ya bashi shi ne ya kore shi daga gonar Iden ya gaya masa ƙasa baza ta ƙara bashi ammfani ba.
  • Allah ya sa lamba a goshin Kayinu wadda alama ce Allah zai kare shi daga kisa daga mutane sa'ad da yake yawo barkatai.

(Hakanan duba: Adamu, hadaya)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • 1 Yahaya 03:12
  • Farawa 04:02
  • Farawa 04:09
  • Farawa 04:15
  • Ibraniyawa 11:4
  • Yahuda 01:11