54 lines
2.8 KiB
Markdown
54 lines
2.8 KiB
Markdown
# ɗaukaka, maɗaukaki, a ɗaukaka, ɗaukakakke, ɗaukakawa
|
|
|
|
## Ma'ana
|
|
|
|
A batu na bai ɗaya kalmar nan "ɗaukaka" tana nufin girmamawa, darajantawa, da matuƙar ban girma. Duk wani abu da ke da ɗaukaka akan ce da shi "maɗaukaki."
|
|
|
|
* A waɗansu lokutan "ɗaukaka" na nufin abin da ke da daraja sosai da kuma muhimmanci. A ɗaya hanun kuma yana nuna daraja ne, mai haske, ko hukunci.
|
|
* Misali batu nan "ɗaukar makiyaya" wanan na nufin wuri mai dausayi inda dabbobinsu ke samu ciyawar ci.
|
|
* Ana amfani da ɗaukaka a hanya ta musammam a ambaci Allah, wanda ya fi kowa da komai ɗaukaka a doron duniya. Kowane abu na baiyana ɗaukakarsa a cikin halaiyarsa da darajarsa.
|
|
* Kalmar nan a "ɗaukaka a kai" tana nufin a yi fahariya da wani abu.
|
|
|
|
Kalmar nan "a ɗaukaka" tana nufin a nuna ko a faɗi yadda girma da muhimmanci na wani abu ko wani mutum. tana nufin a a "bada ɗaukaka."
|
|
|
|
* Mutane kan iya ɗaukaka Allah ta wurin faɗar abubuwan al'ajabi da ya yi.
|
|
* Haka nan za su iya ɗaukaka Allah ta wurin yin rayuwar da ke girmama shi da kuma nuna yadda yake da ɗaukaka.
|
|
* Idan Littafi Mai Tsarki ya ce Allah na ɗaukaka kansa, yana nufin ya baiyana wa mutane girmansa na al'ajabi, mafi yawa ta wurin mu'ujjuza.
|
|
* Allah Uba zai ɗaukaka Allah Ɗa ta wurin baiyana wa mutane cikarsa da darajarsa da girmansa.
|
|
* Duk wanda ya gaskata da Kristi za'a ɗaukaka shi tare da shi. A lokacin dasuka tashia rai za,a canja su su nuna ɗaukakarsa da kuma nunaalherinsa ga dukkan halitta.
|
|
|
|
|
|
Shawarwarin Fassara:
|
|
|
|
* Ya danganta ga wurin, a kwai mabambanta hanyoyi na fassara "ɗaukaka" da suka haɗa da "daraja" ko "mafi haske" ko 'mafi iko" ko "mafi kyau da girma" ko "mafi tsananin daraja."
|
|
* Kalmar nan "maɗaukaki" za'a iya fassara ta da "cikarkiyar ɗaukaka" ko "mai matuƙar martaba" ko "mai tsananin haske" ko "mai matuƙar ban sha'awa da girma."
|
|
* Kalmar nan "bada ɗaukaka ga Allah" za'a iya fassara ta da "girmama girman Allah" ko "yabon Allah sabo da martabarsa" ko "faɗa wa waɗansu yadda girman Allah yake."
|
|
* Kalmar nan "yin ɗaukaka da" za'a iya fassara ta da "yabo" ko "yin fahariyaa cikin" ko "yin taƙama da" ko jin daɗi da."
|
|
* "A ɗaukaka" zai iya zama bada "ɗaukaka ga" ko "a sa a baiyana girma."
|
|
* Kalmar nan "a ɗaukaka Allah" za'a yi fassara ta da "yin magana game da girman Allah" ko "nuna yadda girman Allah yake" ko "girmama Allah ta wurin yi masa (biyayya)."
|
|
* Kalmar nan "ya ɗaukaka" za'a iya fassara ta da nuna cewa "yana da girma sosai" ko a "yaba" ko "a girmama."
|
|
|
|
|
|
(Hakanan duba: ɗauka, biyayya, yabi)
|
|
|
|
|
|
Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:
|
|
|
|
* Fitowa 24:17
|
|
* Littafin Lissafi 14:9-10
|
|
* Ishaya 35:2
|
|
* Luka 18:43
|
|
* Luka 2:9
|
|
* Yahaya 12:28
|
|
* Ayyukan Manzanni 3:13-14
|
|
* Ayyukan Manzanni 7:1-3
|
|
* Romawa 8:17
|
|
* 1 Korintiyawa 6: 19-20
|
|
* Filibiyawa 2:14-16
|
|
* Filibiyawa 4:19
|
|
* Kolosiyawa 3:1-4
|
|
* 1 Tassolonikawa 2:5
|
|
* Yakubu 2:1-4
|
|
* 1 Bitrus 4:15-16
|
|
* Wahayin Yahaya 15:4
|