# ɗaukaka, maɗaukaki, a ɗaukaka, ɗaukakakke, ɗaukakawa ## Ma'ana A batu na bai ɗaya kalmar nan "ɗaukaka" tana nufin girmamawa, darajantawa, da matuƙar ban girma. Duk wani abu da ke da ɗaukaka akan ce da shi "maɗaukaki." * A waɗansu lokutan "ɗaukaka" na nufin abin da ke da daraja sosai da kuma muhimmanci. A ɗaya hanun kuma yana nuna daraja ne, mai haske, ko hukunci. * Misali batu nan "ɗaukar makiyaya" wanan na nufin wuri mai dausayi inda dabbobinsu ke samu ciyawar ci. * Ana amfani da ɗaukaka a hanya ta musammam a ambaci Allah, wanda ya fi kowa da komai ɗaukaka a doron duniya. Kowane abu na baiyana ɗaukakarsa a cikin halaiyarsa da darajarsa. * Kalmar nan a "ɗaukaka a kai" tana nufin a yi fahariya da wani abu. Kalmar nan "a ɗaukaka" tana nufin a nuna ko a faɗi yadda girma da muhimmanci na wani abu ko wani mutum. tana nufin a a "bada ɗaukaka." * Mutane kan iya ɗaukaka Allah ta wurin faɗar abubuwan al'ajabi da ya yi. * Haka nan za su iya ɗaukaka Allah ta wurin yin rayuwar da ke girmama shi da kuma nuna yadda yake da ɗaukaka. * Idan Littafi Mai Tsarki ya ce Allah na ɗaukaka kansa, yana nufin ya baiyana wa mutane girmansa na al'ajabi, mafi yawa ta wurin mu'ujjuza. * Allah Uba zai ɗaukaka Allah Ɗa ta wurin baiyana wa mutane cikarsa da darajarsa da girmansa. * Duk wanda ya gaskata da Kristi za'a ɗaukaka shi tare da shi. A lokacin dasuka tashia rai za,a canja su su nuna ɗaukakarsa da kuma nunaalherinsa ga dukkan halitta. Shawarwarin Fassara: * Ya danganta ga wurin, a kwai mabambanta hanyoyi na fassara "ɗaukaka" da suka haɗa da "daraja" ko "mafi haske" ko 'mafi iko" ko "mafi kyau da girma" ko "mafi tsananin daraja." * Kalmar nan "maɗaukaki" za'a iya fassara ta da "cikarkiyar ɗaukaka" ko "mai matuƙar martaba" ko "mai tsananin haske" ko "mai matuƙar ban sha'awa da girma." * Kalmar nan "bada ɗaukaka ga Allah" za'a iya fassara ta da "girmama girman Allah" ko "yabon Allah sabo da martabarsa" ko "faɗa wa waɗansu yadda girman Allah yake." * Kalmar nan "yin ɗaukaka da" za'a iya fassara ta da "yabo" ko "yin fahariyaa cikin" ko "yin taƙama da" ko jin daɗi da." * "A ɗaukaka" zai iya zama bada "ɗaukaka ga" ko "a sa a baiyana girma." * Kalmar nan "a ɗaukaka Allah" za'a yi fassara ta da "yin magana game da girman Allah" ko "nuna yadda girman Allah yake" ko "girmama Allah ta wurin yi masa (biyayya)." * Kalmar nan "ya ɗaukaka" za'a iya fassara ta da nuna cewa "yana da girma sosai" ko a "yaba" ko "a girmama." (Hakanan duba: ɗauka, biyayya, yabi) Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki: * Fitowa 24:17 * Littafin Lissafi 14:9-10 * Ishaya 35:2 * Luka 18:43 * Luka 2:9 * Yahaya 12:28 * Ayyukan Manzanni 3:13-14 * Ayyukan Manzanni 7:1-3 * Romawa 8:17 * 1 Korintiyawa 6: 19-20 * Filibiyawa 2:14-16 * Filibiyawa 4:19 * Kolosiyawa 3:1-4 * 1 Tassolonikawa 2:5 * Yakubu 2:1-4 * 1 Bitrus 4:15-16 * Wahayin Yahaya 15:4