ha_tw/bible/kt/daughterofzion.md

25 lines
1.1 KiB
Markdown

# ɗiyar Sihiyona
## Ma'ana
"Ɗiyar sihiyona wani salon magane da ke nufin mutanen Isra'ila. An fi amfani da wannan salon maganar a cikin anabce-anabce.
* A cikin Tsohon Alƙawari, ana fin yawn yin amfani da sunan "Sihiyona" a matsayin sunan birnin Yerusalem.
* Ana amfani da "Sihiyona" da Yerusalem" da nufin ambaton Isra'ila.
* Kalmar nan "Ɗiya" ƙauli ne na ƙauna ko tarairaya. Salon magna ne da ke nuna haƙuri da kulawar da Allah ke da su ga mutanensa.
Shawarwarin Fassara:
* Hanyar yin fassara wananya haɗa da "ɗiyata Isra'ila, daga Sihiyona," ko "mutane daga Sihiyona, waɗanda ke kamar ɗiya a gare ni" ko "Sihiyona, ƙaunatattun mutanena Isra'ila."
* Yafi kyau a riƙa moron kalmar "Sihiyona da yake an more ta sosai a cikin Littafi Mai Tsarki. Za a iya ɗan yin rubutu a cikin fassara don a nuna yadda aka mori misalin wata siffa domin a baiyana wata ma'ana ko wani anabci.
* Hakanan ya fi kyau ayi ta moron "Ɗiya" a fassarar waɗanan kalmomin muddun dai an fahimce su da kyau.
(Hakanan duba: Yerusalem, annabi, Sihiyona)
Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:
* Irmiya 06: 02
* Yahaya 12:15
* Matiyu 21:05