ha_tw/bible/names/abraham.md

791 B

Ibrahim, Ibram

Gaskiya

Ibram mutumin Kaldiya ne daga birnin Ur wanda Allah ya zaɓe shi ya zama kakan Isra'ilawa. Allah ya sauya sunansa zuwa "Ibrahim."

  • Ma'anar "Ibram" shi ne "mahaifi da aka ɗaukaka."
  • Ma'anar "Ibrahim" shi ne, "mahaifin masu yawa."
  • Allah ya yiwa Ibrahim alƙawari zai sami zuriya masu yawa, da za su zama babbar al'umma.
  • Ibrahim ya gaskanta Allah ya kuma yi masa biyayya. Allah ya bi da Ibrahim ya tashi daga Kaldiya zuwa ƙasar Kan'ana.
  • Lokacin da suke zama a ƙasar Kan'ana, sa'ad da suka tsufa tukuf, Ibrahim da matarsa Saratu suka sami ɗa, shi ne Ishaku.

(Hakanan duba: Kan'ana, Kaldiya, Saratu, Ishaku)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Galatiyawa 03:08
  • Farawa 11:29-30
  • Farawa 21:04
  • Farawa 22:02
  • Yakubu 02:23
  • Matiyu 01:02