30 lines
1.3 KiB
Markdown
30 lines
1.3 KiB
Markdown
|
# furta, furtawa
|
||
|
|
||
|
## Ma'ana
|
||
|
|
||
|
Furtawa shi ne mutum ya yarda ko ya bayyana cewa wani abu gaskiya ne. "Furtawa" magana ce ko kuma amincewa ne cewa wani abu gaskiya ne.
|
||
|
|
||
|
* Wannan kalma "furta" faɗin gaskiya ne gabagaɗi game da Allah. Zai kuma iya zama bayyana zunubin mu.
|
||
|
* Littafi Mai Tsarki ya ce idan mutane suka furta zunubansu ga Allah, zai gafarta masu.
|
||
|
* Manzo Yakubu ya rubuta a cikin wasiƙarsa cewa idan masu bada gaskiya suka furta zunbansu ga junansu, wannan yana kawo warkaswar ruhaniya.
|
||
|
* Manzo Bulus ya rubuta wa Filibiyawa cewa wata rana kowa zai furta ko yayi shela cewa Yesu Ubangiji ne.
|
||
|
* Bulus kuma ya ce idan mutane suka furta cewa Yesu Ubangiji ne kuma suka gaskata Allah ya tashe shi daga matattu, za su sami ceto.
|
||
|
|
||
|
Shawarwarin Fassara:
|
||
|
|
||
|
* Ya danganta ga yadda ake so a yi amfani da shi cikin rubutu, ga wasu hanyoyin fassara "furtawa" za a iya cewa "yarda" ko "shaidawa" ko "shela" ko "amincewa" ko "tabbatarwa."
|
||
|
* Ga wasu hanyoyi dabam dabam na juya wannan kalma "furtawa" zai iya zama, "furci" ko "shaidawa" ko "magana game da abin da muka gaskata" ko "bayyana zunubi."
|
||
|
|
||
|
(Hakanan duba: bangaskiya, shaida)
|
||
|
|
||
|
Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:
|
||
|
|
||
|
* 1 Yahaya 01:8-10
|
||
|
* 2 Yahaya 01:7-8
|
||
|
* Yakubu 05:5-6
|
||
|
* Lebitikos 05:5-6
|
||
|
* Matiyu 03:4-6
|
||
|
* Nehemiya 01:6-7
|
||
|
* Filibiyawa 02:9-11
|
||
|
* Zabura 038:17-18
|