\v 4 Kaito! Al'umma, masu zunubi, mutanen da zunubi ya danne su ƙasa, zuriyar masu aikata mugunta, 'ya'ya masu aikin lalata! Sun yi watsi da Yahweh, sun rena Mai Tsarki na Isra'ila, sun ware kansu daga gare shi.
\v 6 Tun daga tafin sawu har zuwa kai ba inda ba ciwo; sai ciwuka ne da ƙoƙƙojewa, da sababbin raunuka; ba'a rufe su ba, ba'a tsabtace su ba, ba'a naɗe su ba, ko kuma a sa masu mai.
\v 11 "Mene ne yawan hadayunku a gare ni?" in ji Yahweh. Ina da isassun baye-bayen ƙonawa na raguna, da kitsen manyan dabbobi; da jinin bijimai, da raguna, ko awaki waɗanda bana jin daɗi.
\v 13 Kada ku ƙara kawo baye-bayenku marasa ma'ana, na ƙi ƙonennan turare, ba zan yarda da bukukuwanku na sabon wata ba da na Asabaci - Ba zan yarda da wannan taron ba.
\v 15 Don haka lokacin da kuka buɗe hannuwanku kuna addu'a na ɓoye fuskata daga gare ku; koda ya ke kun yi addu'o'i da yawa, Ba zan ji ba; hannuwanku sun cika da jini.
\v 18 Sai ku zo mu tattauna tare," in ji Yahweh; koda zunubanku sun yi kamar jangarura za su yi fari kamar ƙanƙara; koda sun yi jawur kamar jini, za su zama kamar ulun auduga.
\v 23 Sarakunanki masu tayarwa ne da kuma abokan ɓarayi; kowa na ƙaunar cin hanci, yana gudu domin ya ci haram. Ba su kare marayu ba, ba su kuma yiwa gwauruwa shari'ar adalci ba a lokacin da ta zo gare su.
\v 24 Saboda haka sai ku ji abin da Yahweh mai runduna ya faɗi, Mai Iko na Isra'ila: "Kaiton su! Zan ɗauki fansa a kan maƙiyana, in kuma nuna ramuwata a kan magabtana;
\v 2 Zai zamana a kwanaki na ƙarshe za a kafa tsaunin gidan Yahweh a can ƙololuwar tsaunuka, za a tada shi bisa dukkan tuddai, dukkan al'ummai kuma za su kwararo gare shi.
\v 3 Mutane da yawa za su zo su ce, "Ku zo mu je kan tsaunin Yahweh, zuwa gidan Allah na Yakubu, don ya koya mana waɗansu hanyoyinsa, mu kuma yi tafiya cikin tafarkunsa." Gama daga Sihiyona shari'a za ta fito maganar Yahweh kuma daga Yerusalem.
\v 4 Zai hukunta tsakanin al'ummai ya kuma yanke shawara ga mutane da yawa; za su mayar da takkubansu garemani, mãsunsu kuma su maida su almakashin yanke rassa; al'umma ba za ta sake tayar da takobi gãba da al'umma ba, ko kuma su sake horar da kansu don yaƙi.
\v 6 Gama ka yi watsi da mutanenka, gidan Yakubu, saboda sun cika da al'adu daga gabas suna kuma karatun sihiri kamar Filistiyawa, suna kuma shan hannuwa da 'ya'yan băƙi.
\v 19 Mutane za su shiga kogonnin duwatsu da kuma ramummuka a ƙasa, domin ɓuya daga razanar Yahweh, da kuma darajar ɗaukakarsa, a lokacin daya tashi domin ya razana duniya.
\v 20 A ranar nan mutane za su watsar da gumakansu na azurfa da zinariya da suka yiwa kansu domin su bauta masu - za su watsar da su a gidan mujiya da jemagu.
\v 21 Mutane za su shiga cikin matsin duwatsu da kuma cikin tsagar fasassun duwatsu domin su ɓuya daga hasalar Yahweh, kuma daga darajar martabarsa, a lokacin da ya tashi domin ya razana duniya.
\v 9 Suka duba shaidunsu a fuskarsu suna gãba da su; suna maganar zunubansu kamar Sodom; ba su ɓoye shi ba. Kaiton su! Gama sun kammalawa kansu bala'i.
\v 12 Mutanena 'ya'yansu su ne masu wahalshe su, mata ne kuma ke mulkinsu. Mutanena masu yi maku jagora suna ɓatar da ku suna kuma rikitar da hanyar tafarkinku.
\v 24 A maimakon ƙanshin turare za su yi wari; a maimakon sarƙa kuma igiya; a maimakon gyararriyar suma kuma saiƙo, a maimakon sutura mai ƙawa kuma kayan makoki; tsaga maimakon kyau.
\v 26 Ƙofofin Yerusalem za su yi makoki da baƙinciki; za ta kuma zauna a ƙasa a kaɗaice.
\c 4
\cl Sura 4
\p
\v 1 A wannan rana mata bakwai za su riƙe namiji ɗaya su ce, "Mă ciyar da kanmu, mu yiwa kanmu suturar da za mu sa. Amma ka yarda a kira mu da sunanka domin a kawar mana da kunya."
\v 2 A wannan ranar rassan Yahweh za suyi kyau da kuma ɗaukaka, 'ya'yan itatuwan ƙasar kuma za su yi zaƙi, da kuma jin daɗi ga waɗanda suka ragu a Isra'ila.
\v 3 Zai kasance a wannan ranar da wanda ya ragu a Sihiyona da kuma wanda ya ragu a Yerusalem za a kira shi mai tsarki, da kuma duk wanda aka rubuta sunansa a matsayin mazaunin Yerusalem.
\v 4 Wannan zai faru a lokacin da Ubangiji zai share tsaurin idon 'yan matan Sihiyona, ya kuma goge jinin da ya manne daga tsakiyar Yerusalem, ta wurin ruhun hukunci da kuma ruhun harshen wuta.
\v 5 Sa'an nan dukkan sassan Tsaunin Sihiyona da kuma kan wuraren taruwarta, Yahweh zai yi girgije da hayaƙi da rana, da kuma hasken harshen wuta da dare; zai zama inuwa a kan dukkan ɗaukaka.
\v 6 Za ta bada inuwa da rana daga zafi, da kuma mafaka da kuma maɓoya daga hadari da ruwan sama.
\c 5
\cl Sura 5
\p
\v 1 Sai in raira waƙa ga ƙaunataccena, waƙar ƙaunataccena game da garkar inabinsa. Wadda nake ƙauna sosai yana da garka a tudu mai dausayi.
\v 2 Ya gyara ta, ya cire duwatsu, ya kuma shuke ta da irin inabi mai matuƙar daraja. Ya gina hasumiya a tsakiyar gonar, ya kuma kafa wurin matse ruwan inabi. ya jira ta bada 'ya'ya amma sai 'ya'yan inabin jeji kawai ta yi.
\v 6 Zan watsar da ita, ba zan yi mata noma ko kaftu ba. A maimakon haka ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su tsiro a cikin ta. Zan kuma umarci giza-gizai kada su yi ruwa a kanta.
\v 7 Domin garkar inabin Yahweh mai runduna ita ce gidan Isra'ila, mutanen Yahuda kuma dashensa ne da ya ke jin daɗi; ya jiraci adalci, a maimakon haka sai kisa; a maimakon adalci kuma, sai ihun neman taimako.
\v 8 Kaiton su masu yawo gida gida, waɗanda ke haɗa wurare daga wannan wuri zuwa wancan wuri, har sai ba ɗakunan da suka ragu sai kai kaɗai za a bari a cikin ƙasar!
\v 12 Suna shagali da sarewa da garaya da tambari da algaita da ruwan inabi, amma ba su fahimci aikin Yahweh ba Ba su kuma yi la'akari da aikin hannuwansa ba.
\v 14 Domin haka Lahira ta maida marmarinta babba ta kuma buɗe bakinta sosai; da masanansu da mutanensu da shugabanninsu da masu duba na cikinsu da kuma waɗanda ke murna a cikin su, sun ɗunguma Lahira.
\v 19 Kaiton masu cewa, "Bari Allah ya yi sauri, bari ya hanzarta ya yi aikinsa, domin mu ga ya faru; kuma bari shirye-shiryen Mai Tsarki na Isra'ila su zo, domin mu sansu."
\v 24 Saboda haka kamar yadda harshen wuta ke lanƙwame kututture, kamar kuma yadda busasshiyar ciyawa ke shiga harshen wuta haka saiwarsu za ta mutu, kyansu kuma ya gushe kamar ƙura. Wannan zai faru saboda sun ƙi shari'un Yahweh mai runduna, saboda kuma sun rena maganar Mai Tsarki na Isra'ila.
\v 25 Saboda haka fushin Yahweh yana kan mutanensa. Ya miƙa hannusa gãba da su ya kuma hore su. tsaunuka sun razana, gawawwakinsu sun zama kamar sharar da a ka zubar a bakin hanyonyi. A cikin duk waɗannan abubuwa fushinsa bai sauka ba; a maimakon haka hannunsa har yanzu yana miƙe.
\v 29 Gurnaninsu kuma kamar na zãki; za su yi ruri kamar matasan zãki. Za su yi ruri su fizge abin da suka farauto su kuma ja shi su tafi, ba kuma wanda zai kuɓutar da su.
\v 30 A wannan ranar za su yi ruri kamar yadda tekuna ke ruri. In wani ya dudduba ƙasar zai ga duhu da shan wuya; ko ma da haske za a mai da shi duhu ta wurin giza-gizai.
\c 6
\cl Sura 6
\p
\v 1 A cikin shekarar da sarki Uziya ya mutu, na ga Ubangiji zaune a kan kursiyi; yana da tsayi da kuma martaba, gezar tufarsa kuma ta cika haikalin.
\v 2 A sama da shi kuma da serafim; kowannen su yana da fuka-fukai shida; kowannen su yana rufe fuska da guda biyu, ya kuma rufe ƙafafu da guda biyu, yana kuma shawagi da guda biyu.
\v 3 Suna kiran juna suna cewa, "Mai Tsarki, Mai Tsarki, Mai Tsarki," shi ne Yahweh mai runduna! Dukkan duniya ta cika da ɗaukakarsa."
\v 5 Sa'an nan na ce "kaitona! Gama na hallaka domin ni mutum ne dake da leɓuna marasa tsarki, ina kuma rayuwa a cikin mutane marasa tsarkin leɓuna, saboda idanuna sun ga Sarki, Yahweh, Yahweh mai runduna!"
\v 10 Mai da zuciyarsu ta zama marar tunani, kunnuwansu kuma su kurmance, idanunsu kuma su makance. A maimakon haka za su iya gani da idanunsu, su ji da kunnuwansu, su kuma fahimta da zuciyarsu, kuma daga nan su juyo su kuma warke."
\v 11 Sai na ce Ubangiji har tsawon wanne lokaci? '"Ya amsa "Har sai birane sun zama kangaye ba mazauna a ciki, gidaje kuma sun zama ba mutane, ƙasar kuma ta zama yasasshiya,
\v 13 Koda kashi ɗaya cikin goma na mutanen suka ragu a cikinsa, duk da haka za a ƙara hallaka shi; zai zama kamar ranar da aka datse itacen rimi wanda gungumensa ya ragu, iri mai tsarki na cikin kututture."
\c 7
\cl Sura 7
\p
\v 1 A kwanakin Ahaz ɗan Yotam ɗan Uziya, sarkin Yahuda, Rezin na Aram da Feka ɗan Remaliya da sarkin Isra'ila, suka je Yerusalem domin su yaƙe ta, amma ba su iya yin nasara da ita ba.
\v 2 Sai aka sanar da gidan Dauda cewa Aram ya haɗa kai da Ifraim. Sai ya tsorata, haka ma zuciyar mutanensa, kamar yadda itatuwan jeji ke kaɗawa a cikin iska.
\v 3 Sai Yahweh yace da Ishaya, "Ka tafi tare da ɗanka Shiya-Yashub ku sadu da Ahaz a ƙarshen kwararon babban wurin da aka datse ruwa, a kan hanya zuwa Filin masu wanki da guga.
\v 4 Ka ce da shi, 'Ka lura, ka tsaya a natse, kada ka ji tsoro ko ka razana saboda waɗannan 'yan guma-gumai na wuta, ta wurin zafin fushin Rezin da Aram, da Feka ɗan Remaliya.
\v 5 Aram, Ifraim da ɗan Remaliya sun ƙulla mugun abu găba da kai; sun ce,
\v 6 "Bari mu kai wa Yahuda hari mu firgita ta, mu kuma fasa cikinta mu naɗa sarkinmu a can, wato ɗan Tabil."
\v 8 saboda shugabar Aram ita ce Damaskus, shugabar Damaskus kuma ita ce Rezin. Cikin shekaru sittin da biyar, za'a watsa Ifraim kuma ba za su zama al'umma ɗaya ba
\v 9 Shugabar Ifraim ita ce Samariya, shugaban Samariya kuma shi ne ɗan Remaliya. Idan ba ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya ba, tabbas ba za ku zama da kariya ba.""'
\v 11 "Ka roƙi alama daga Yahweh Allahnka; ka yi roƙonta ko a cikin zurfafa ko a can sama."
\v 12 Amma Ahaz yace "ba zan yi tambaya, ko kuma in gwada Yahweh ba."
\v 13 Domin haka Ishaya ya amsa, "Ku saurara, gidan Dauda. Ya ku mutane ashe bai isheku ba ku gwada haƙurin jama'a? Dole ne kuma ku gwada haƙurin Allahna?
\v 14 Saboda haka Ubangiji da kansa zai ba ku alama, duba budurwa za ta yi juna biyu za ta haifi ɗa, za a kira sunansa Imanuwel.
\v 15 Zai ci fãra da ruwan zuma a lokacin da ya ƙi mugunta ya kuma zaɓi nagarta.
\v 16 Gama kafin yaron ya san ƙin mugunta da zaɓar nagarta, ƙasar sarakunan nan guda biyu da kuka ji tsoronsu za ta zama kufai.
\v 17 Yahweh zai sauko maku da wata rana a kan mutanenku da gidan mahaifanku ranar da ba a taɓa ganin ta ba tun da Ifraim ya bar Yahuda - zai aiko maku da sarkin Asiriya."
\v 20 A wannan lokacin Ubangiji zai yi aski da rezar da aka yi haya daga hayin Kogin Yuferitis - sarkin Asiriya - da kai da gashin ƙafafu; za a kuma share gemu.
\v 21 A wannan rana mutum zai yi kiwon 'yar karsana da tumaki guda biyu,
\v 22 Kuma saboda yalwar madarar da za su bayar, zai ci cuku, ga duk waɗanda suka ragu a ƙasar za su ci cuku da ruwan zuma.
\v 23 A wannan lokacin, a inda a kwai dubu na inabi da ya kai azurfa dubu, a wurin ba za a ga komai ba sai sarƙarƙiya da ƙayayuwa.
\v 24 Mutane za su fita farauta da bãka, saboda dukkan ƙasar za ta cika da ƙaya da sarƙaƙiya.
\v 25 Za su tsaya nesa da dukkan tuddan da aka nome da fartanya, domin tsoron sarƙaƙiya da ƙayayuwa; amma zai zama wurin da dabbobi da tumaki za su yi kiwo.
\c 8
\cl Sura 8
\p
\v 1 Yahweh yace mani, "Ka ɗauki babban allo ka yi rubutu a kansa, 'Maha-Shalal-Hash-Baz.'
\v 2 Zan kira amintattun shaidu su tabbatar mani, Yuriya Firist, da Zakariya ɗan Yebirekiya."
\v 3 Na je wurin annabiya, ta kuwa yi juna biyu ta haifi ɗa. Sai Yahweh yace mani, "Ka kira sunansa 'Maha-Shalal-Hash-Baz.'
\v 4 Gama kafin yaron ya san yin kuka har ya furta, 'Babana da Mamata,' sarkin Asiriya zai kwashe dukiyar Damaskus da ganimar Samariya."
\v 7 don haka Ubangiji ya kusa kawo ruwayen Kogi a kansu, masu ƙarfi da yawa, sarkin Asiriya da dukkan ɗaukakarsa. Za ya hau kan dukkan magudanansa ya yi ambaliya kan iyakokinsa.
\v 9 Ku mutanen za a daddatsa ku gunduwa-gunduwa. Ku saurara, dukkan ku manisantan ƙasashe: ku yi ɗammara domin yaƙi za a kuwa daddatse ku, ku yi shiri za a kuwa gutsuttsuraku.
\v 14 Zai zama wuri maitsarki; amma zai zama dutse abin bugu da pã abin sa tuntuɓe ga dukan gidajen Isra'ila, zai zama tarko da azargiya ga mutanen Yerusalem.
\v 18 Duba, Ni da 'ya'yan da Yahweh ya bani domin alamu ne da al'ajibai cikin Isra'ila daga Yahweh mai runduna, wanda ya ke zaune akan Tsaunin Sihiyona.
\v 19 Za su ce maku, "Ku tuntuɓi mãsu duba da bokaye" waɗanda suke kashe murya suna surkulle. Shin ko mutane ba za su tuntuɓi Allahnsu ba? za su tuntuɓi matattu a madadin masu rai?
\v 20 Ga shari'a da kuma shaida! idan ba su faɗi waɗannan abubuwan ba, saboda ba bu hasken wayewar gari a garesu.
\v 21 Za su ratsa ta cikin ƙasa da babbar damuwa da yunwa. Idan suna jin yunwa, za su yi fushi su la'anta sarkinsu da Allahnsu, yayin da suka ɗaga fuskokinsu sama.
\v 22 Za su du bi duniya kuma za su ga wahala, duhu, da azabtarwa. Za a koresu zuwa cikin ƙasar duhu.
\c 9
\cl Sura 9
\p
\v 1 Amma za a kawar da baƙin duhun daga wurin ta wadda take cikin azaba a dã. A kwanakin da ya ƙasƙantar da ƙasar Zebulun da ƙasar Naftali, amma cikin kwanaki na ƙarshe zai ɗaukakata, ta hanyar teku, ƙetaren Yodan, Galili ta al'ummai.
\v 3 Ka riɓanya al'umma; ka ƙara farincikin su. Suna murna gaban ka kamar murna a lokacin girbi, kamar yadda mutane suke murna sa'ad da suke raba ganima.
\v 6 Gama a gare mu an haifi yaro, a gare mu an bada ɗa; mulki kuma zai kasance a kafaɗarsa; za a kira sunansa Al'ajibi Maishawara, Allah maigirma, Uba Madawwami, Sarkin Salama.
\v 7 Ƙaruwar mulkinsa da salama bata da iyaka, ya yin da ya ke mulki kan kursiyin Dauda, da bisa mulkinsa, a kafa shi a kuma tabbatar dashi cikin gaskiya da adalci daga wannan lokaci har abada kuma. Himmar Yahweh Mairunduna zai yi wannan.
\v 12 Suriyawa daga gabas, da kuma Filistiyawa daga yamma. Da baki buɗe za su cinye Isra'ila. A cikin waɗannan duka, fushinsa bai juya ba; maimakon haka, hannunsa har yanzu a miƙe ya ke.
\v 17 Domin wannan Ubangiji ba za ya yi murna da majiya karfinsu ba ba kuma zai tausayawa marayunsu da gwaurayensu ba, domin kowannensu marasa allahntaka ne da masu aikata mugunta, kowanne baki kuma yana faɗin wauta. Cikin waɗannan duka fushinsa ba zai juya ba; maimakon haka, hannunsa har yanzu a miƙe ya ke.
\v 20 Za su fizge abinci a hannun dama duk da haka za su ji yunwa, za su ci abinci a hannun hagu duk da haka ba za su ƙoshi ba. Kowanne zai ci naman dantsen hannunsa.
\v 21 Manasse zai lanƙwame Ifraim, Ifraim kuma Manasse, tare kuma za su kaima Yahuda farmaki. Cikin waɗannan duka, fushinsa yana nan, maimakon haka, har yanzu hannunsa a miƙe ya ke.
\c 10
\cl Sura 10
\p
\v 1 Kaitonsu waɗanda ke zartar da hukuncin zalunci suke rubuta umarnan rashin gaskiya.
\v 4 Ba abin daya rage, za ku laɓe ƙarƙashin 'yan sarƙa, ko ku faɗi tsakanin kisassu. Cikin dukkan waɗannan abubuwa, fushinsa ba zai sauka ba; maimakon haka, har yanzu hannunsa a miƙe ya ke.
\v 6 Na aike shi gãba da al'umma mai girmankai, gãba da mutane masu ɗauke da ambaliyar fushina. Na umarce shi ya ɗauki ɓãtattu, ya kwashi ganima, ya tattake su kamar laka cikin tituna.
\v 12 Sa'ad da Ubangiji ya gama aikin sa akan Tsaunin Sihiyona da bisa Yerusalem, zan hukunta jawabin faɗin ran sarkin Asiriya da homarsa.
\v 13 Domin yace, "Da karfina da hikimata Na yi aiki. Ina da fahimta, na kuma kawas da iyakoki na mutane. Na sace taskokin su, kamar sã na nakasadda mazauna nan wurin.
\v 14 Hannuna ya tsaya, kamar sheƙa, dukiyar dangogi, kuma kamar wanda ya tattara ƙwan da aka ƙyale. Na tattaro dukkan duniya. Ba bu wanda ya motsa fiffike, ko ya buɗe baki balle suyi ƙara."
\v 15 Ko gatari zai iya yiwa mai sara da shi alfahari? ko zarto zai iya ɗaukaka kansa bisa wanda ya ke yanka da shi? sai kace sanda zata iya ɗaga mai ɗaukar ta, ko kuma kulkin katako zai ɗaga mutum.
\v 20 A wannan rana, ringin Isra'ila, da iyalin Yakubu waɗanda suka tsira, ba za su dogara ga wanda ya ci nasara da su ba, amma lallai za su dogara ga Yahweh, MaiTsarkin nan na Isra'ila.
\v 22 Ko da shike mutanenka, Isra'ila, suna kama da yashin teku, sai ringi daga cikin su za su komo. An zartar da dokar Hallakarwa, kamar yadda adalci mai malalowa ya wajabta.
\v 24 Domin wannan Ubangiji Yahweh mai runduna yace, "Mutanena da suke zaune cikin Sihiyona, kada ku ji tsoron Asiriyen. Zai buge ku da sanda ya ɗaga kerensa ga bada ku, kamar yadda Masarawa suka yi.
\v 25 "Kada ku ji tsoron sa, gama a cikin ɗan lokaci kaɗan fushina a kanku zai ƙare, fushi na zai kai ga hallakarwarsa."
\v 26 Daga nan Yahweh mai runduna zai tayar da bulala akansu, kamar yadda ya fatattaki Midiyan a Tsaunin Oreb. Zai ɗaga sandarsa bisa teku ya ɗaga ta sama kamar yadda ya yi a Masar.
\v 3 Marmarin sa zai kasance tsoron Ubangiji; ba zaiyi shari'a bisa ga abin da idanunsa suka gani ba, ba kuwa zai yi hakunci bisa ga abin da kunnensa ya ji ba.
\v 4 Maimakon haka zai shar'anta talakwa bisa ga adalci bisa ga dai-daita kuma zai yanke shawara ga masu tawali'u na duniya. Zai bugi duniya da sandar bakinsa, da numfashin leɓunansa kuma zai kashe miyagu.
\v 6 Kyarkeci zai zauna tare da rago, damisa kuma zata kwanta tare da ɗan'akuya, ɗan maraki da ɗan zaki tare da kiwataccen ɗan maraƙi, za su zauna tare, ɗan yaro kuwa zai bishe su.
\v 10 A wannan rana, tushen Jesse zai tsaya a matsayin tuta ga mutane. Al'ummai za su neme shi, wurin hutun sa kuma zai zama abin ɗaukaka.
\v 11 A wannan rana, Ubangiji zai sake sa hannunsa domin ya fanshi sauran mutanensa da suka rage a Asiriya, Masar, Fatros, Kush, Ilam, Shina, Hamat, da tsibirai na teku.
\v 13 Zai juyar da kishin Ifraim, masu azabtar da Yahuda kuma zai datse su. Ifraim ba zai yi kishin Yahuda ba, Yahuda kuma ba zai ƙara kishin Ifraim ba.
\v 14 Maimakon haka zasu sauko bisa tuddan Filistiyawa a wajen yamma, tare za su washe 'ya'yan gabas. Za su kai hari ga Idom da Mowab Mutanen Ammon kuma za su yi masu biyayya.
\v 15 Yahweh zai hallakar da dukkan kwarurruka na Tekun Masar. Da iskarsa mai ƙonewa zai karkaɗe hannunsa bisa kan Kogin Yufiretis zai raba su zuwa rafuffuka bakwai, domin a iya ƙetarewa da takalmi a ƙafa.
\v 16 Zai kasance akwai karabka domin sauran mutanensa, waɗanda suka ragu za su dawo daga Asiriya, kamar yadda akayi ga Isra'ila cikin ranar da suka taso daga ƙasar Masar
\c 12
\cl Sura 12
\p
\v 1 A wannan rana za ka ce, "Zan gode maka, Yahweh. Koda shike ka yi fushi da ni, fushinka ya juya, ka kuwa yi mani ta'aziya.
\v 4 A wannan rana za ku ce, "Kuyi godiya ga Yahweh ku kuma kira ga sunansa; ku bayyana ayyukan sa a wurin al'ummai, ku yi shelar sunansa maɗaukaki ne.
\v 4 Hayaniyar mutane cikin duwatsu, sai kace na mutane da yawa! Hayaniya ta mulkokin al'ummai a tattare! Yahweh mai runduna yana tattara runduna domin yaƙi.
\v 8 Za su firgita; zafi da baƙinciki za su kama su, kamar mace cikin naƙuda. Za su dubi junansu cikin mamaki, fuskokinsu za su zama kamar gaushen wuta.
\v 11 Zan hori duniya domin muguntarta da Miyagu domin zunubansu. Zan kawo ƙarshen alfarmar masu girmankai in ƙasƙantar da alfarmar mutane masu ban tsoro.
\v 13 Domin wannan zan sa sammai su yi rawar jiki, duniya kuma za ta girgiza ta gusa daga wurinta, ta wurin hasalar Yahweh mai runduna, da cikin ranar fushinsa mai zafi.
\v 20 Ba za a zauna ciki ko rayuwa a ciki ba daga tsara zuwa tsara. Balarabe ba zai kafa rumfarsa a can ba, makiyaya kuma ba za su bar garken su su huta a can ba.
\v 22 Kuraye za su yi kuka a cikin kagarorinsu, diloli kuma a cikin fadodinsu masu kyau. Lokacinta ya kusa, kwanakinta kuma ba za a jinkirtasu ba.
\c 14
\cl Sura 14
\p
\v 1 Yahweh zai ji tausayin Yakubu; zai sake zãɓen Isra'ila ya sake dawo da su cikin ƙasarsu, bãƙi za su haɗa kai da su, za su haɗa kansu da gidan Yakubu.
\v 2 Al'ummai za su ɗauke su su kai su garinsu. Gidan Isra'ila zai ɗauke su ya kai su ƙasar Yahweh a matsayi bayi maza da mata. Za su bautadda waɗanda suka kwashe a dã, za su yi mulkin waɗanda suka ƙuntata masu.
\v 8 Har itatuwan sayfres suna murna da kai tare da Sidas na Lebanon; suka ce, 'Tunda aka ƙasƙantar da kai, ba bu wani mai saran itace da ya zo ya sare mu ƙasa.'
\v 9 Lahira daga ƙasa na marmarin saduwa da kai idan ka je can. Ta tayar da mattatu domin ka, dukkan sarakunan duniya an sa sun tashi daga kursiyinsu, dukkan sarakunan al'ummai.
\v 13 Sai ka ce a cikin zuciyarka, 'Zan hau cikin sama, Zan ɗaukaka kursiyina bisan taurarin Allah, zan zauna bisa tsaunin taruwar jama'a, cikin ƙarshen arewa.
\v 19 Amma kai an jefar da kai can waje da kushewarka kamar reshen da a ka jefar. Mattatu sun rufe ka kamar riga, waɗanda a ka sara da takobi, masu gangarowa zuwa ramin duwatsu.
\v 25 Zan karya mutumin Asiriya cikin ƙasa ta kuma bisa kan duwatsu zan tattake shi ƙarƙashin sawu. Daga nan za a kawar da karkiyarsa daga gare su kayansa kuma daga kafaɗarsu."
\v 29 Kada ku yi murna, dukkan ku Filistiyawa, cewa sandar da ya buge ki ya karye. Gama daga cikin tsatson maciji ƙasa mai dafi za ta fito, zuriyarsa kuma za ta zama wuta mai firiyar maciji.
\v 31 Ki yi kururuwa, ƙofa, ki yi kuka, birni, dukkan ku za ku narke, Filistiya. Gama daga arewa girgije mai hayaƙi ke fitowa, ba kuma mai ratsewa cikin dagarsa.
\v 1 Furci game da Mowab. Lallai, a dare ɗaya Ar ta Mowab ta zama marar amfani an hallaka ta, Lallai, a dare ɗaya Kir ta Mowab ta zama marar amfani an hallaka ta.
\v 2 Sun hau saman masujada, mutanen Dibon sunje sammai don su yi kuka; Mowab na makoki kan Nebo da Medeba. Duk kawunansu an aske su kwal duk gemunsu kuma an yanke su.
\v 4 Heshbon da Ileyale sun yi kira domin taimako; a na jin muryarsu har Yahaz. Domin haka mayaƙa na Mowab suna kira domin neman taimako; su kadai suna rawar jiki.
\v 5 Zuciyata tana kuka domin Mowab; sanannun ta suna gudu zuwa Zowa da Iglat Shelishiya. Sun hau zuwa wajen Luhit suna kuka; hanyar zuwa Horonayim sun tada murya da ƙarfi kan hallakarsu.
\v 9 Domin ruwayen Dimon cike suke da jini; amma zan kawo wanda ya fi zafi akan Dimon. Zaki zai kai hari ga waɗanda suka tsira a Mowab da kuma sauransu da suka rage a cikin ƙasar.
\c 16
\cl Sura 16
\p
\v 1 Ku aika da raguna domin mulkin ƙasa daga Selah cikin jeji; zuwa tsaunin ɗiyar Sihiyona.
\v 4 Ka barsu su zauna a cikin ku, 'yan gudun hijira daga Mowab; ka zama maɓuya gare su daga mai lalatarwa." Gama zalunci zai tsaya, hallakarwa kuma zata tsaya, waɗannan da suke tattaka mutane za su ɓace a ƙasar.
\v 5 A cikin alƙawarin aminci kuma za'a kafa kursiyi, ɗaya kuma daga cikin rumfar Dauda da aminci zai zauna can, zai yi shari'a yana neman adalci, yana aikata gaskiya.
\v 8 Gonakin Heshbon sun bushe duk da kuringar inabin Sibma. Sarakunan al'ummai sun tattake zaɓaɓɓun inabin da suka kai zuwa Yaza, da suka yaɗu zuwa cikin jeji. Rassanta sun yaɗu waje; sun fita zuwa ƙetaren teku.
\v 9 Domin wannan zan yi kuka tare da Yaza domin kuringar Sibma. Zan dausayar da ku da hawaye na, Heshbon da Ileyale. Gama na kawo ƙarshen farincikinku game da amfanin gonakinku damina da na kaka.
\v 10 Murna da farincikinku an ɗauke su daga 'ya'yan itatuwan kuramenku, ba sauran waƙa, ba sowa cikin gonakinku. Ba mai taka ruwan inabi a wurin matsewa, gama na kawo ƙarshen sowa ga mai takawar.
\v 13 Wannan ita ce maganar da Yahweh ya faɗi game da Mowab da farko.
\v 14 Yahweh ya sake yin magana, "Cikin shekara uku, ɗaukakar Mowab za ta ɓace; duk da yawan mutanensa, sauran da za su ragu za su zama 'yan kaɗan marasa amfani."
\v 3 Biranensu masu kagara za su ɓace daga Ifraim, mulki kuma daga Damaskus, da ringin Aram - za su zama kamar ɗaukakar mutanen Isra'ila - wannan furcin Yahweh mai runduna ne.
\v 6 Za'a bar kala, duk da haka, kamar lokacin da itacen zaitun ke kakkaɓewa: biyu ko uku cikin reshe mafi bisa, huɗu ko biyar a cikin rassa mafi bisa na itace mai 'ya'ya - wannan furcin Yahweh ne, Allah na Isra'ila.
\v 9 A wannan rana ƙarfafan biranensu za su zama kamar wuraren da aka bar su kufai cikin kurmi a ƙwanƙolin tsaunuka, da aka bar su saboda mutanen Isra'ila wannan zai zama hallaka.
\v 10 Domin kun manta da Allah mai cetonku, kun kuma yi watsi da dutsen ƙarfinku. Kuna dasa tsire-tsiren da suka gamshe ku, kuna dasa rassan inabi da kuka karɓa wurin baƙo,
\v 11 A cikin rana kayi dashe da shinge da noma. Bada daɗewa ba irinka zai yi girma, amma girbinka zai gaza a cikin ranar baƙinciki da matsananciyar azaba.
\v 13 Al'ummai za su yi ruri kamar gudun ruwaye masu yawa, amma Allah zai tsauta masu. Za su gudu nesa za'a runtume su kamar ƙai-ƙai a kan tsaunuka gaban iska, kamar guguwa kuma gaban hadari.
\v 2 Wadda take aika jakadu ta hanyar teku, a cikin ruwaye ta jiragen iwa Ku tafi ku, jakadu masu sauri, wurin dogayen al'ummai masu taushin fata, wurin mutanen da a ke tsoron su nesa da kusa, al'umma mai ban razana mai tattakewa, wadda ruwaye sun raba ƙasarta.
\v 5 Kafin girbi, ya zo sa'ad da fure ya kaɗe, huda tana zama nunannun 'ya'yan inabi, zai datse maɓulɓula da ƙugiya mai tsini, zai sare ya kuma kwashe rassan da suka barbaje.
\v 6 Za a bar su tare saboda tsuntsayen duwatsu da dabbobin duniya. Tsuntsaye za su yi damina a kansu, kuma dukkan dabbobin duniya za su yi lokacin sanyi a kansu."
\v 7 A wancan lokacin dogayen mutane masu taushin jiki za su kawo hadaya ga Yahweh, daga mutanen da a ke tsoro nesa da kusa, ƙarfafan al'ummai masu ban razana, waɗanda rafuka suka raba ƙasarsu, zuwa wurin da ya ke na sunan Yahweh mai runduna, zuwa Tsaunin Sihiyona.
\c 19
\cl Sura 19
\p
\v 1 Furci game da Masar. Duba, Yahweh ya hau girgije mai sauri ya taho Masar; gumakan Masar za su razana a gabansa, zuciyar masarawa za ta narke a cikin su.
\v 2 "Zan haɗa masarawa gãba da masarawa: Mutum zai yi faɗa gãba da ɗan'uwansa, mutum gãba da maƙwabcinsa; birni kuma gãba da birni, mulki kuma gãba da mulki.
\v 3 Ruhun Masar zai karaya daga ciki. Zan rushe shawararsa, koda ya ke sun nemi shawarar gumakai, da ruhun matattu, da masu duba, da masu aiki da ruhohi.
\v 11 Sarakunan Zowan wawaye ne gaba ɗaya. Shawarar mashawartan Fir'auna mafiya wayo ta zama rashin hankali. Yaya za ka iya cewa da Fir'auna, "Ni ɗan mutane masu hikima ne, ni ɗan sarakunan dã ne?"
\v 16 A wannan rana, Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki da tsoro saboda ɗagaggen hannun Ubangiji mai runduna a kansu.
\v 17 Ƙasar Yahuda za ta zama sanadin tangaɗin Masar. Dukkan sa'ad da wani ya tuna masu da ita, za su ji tsoro, saboda shirin Yahweh, kan abin da ya ke shiryawa gãba da su.
\v 18 A wannan rana za a sami birane biyar cikin ƙasar Masar da za su yi magana da harshen Kan'ana su yi rantsuwa su yi amana da Yahweh mai runduna. Ɗaya daga waɗannan za a kira shi Birnin Rana.
\v 19 A wannan rana za a sami bagadin Yahweh a tsakiyar ƙasar Masar, da dutsen daya zama ginshiƙi na kan iyakar Yahweh.
\v 20 Zai zama kamar alama da shaida ga Yahweh mai runduna a cikin ƙasar Masar. Idan suka yi kuka ga Yahweh saboda mai tsananta masu, zai aiko masu da mai ceto da mai kariya, zai kuma cece su.
\v 21 Yahweh zai zama sananne a Masar, a wannan rana Masarawa za su san da kasancewar Yahweh. Za su yi sujada da hadayu da baye-baye, za su yi wa'adodi ga Yahweh, su cika su kuma.
\v 22 Yahweh zai azabci Masar, yana azabtarwa da warkarwa kuma. Za su juyo ga Yahweh; zai ji addu'arsu ya warkar dasu.
\v 23 A wannan rana za a sami karabka tsakanin Masar da Asiriya, Asiriye zai zo Masar, Bamasare kuma zai je Asiriya; Masarawa kuma za su yi sujada tare da Asiriyawa.
\v 24 A cikin wannan rana, Isra'ila za ta zama ta uku tare da Masar da Asiriya, za su zama albarka a tsakiyar duniya;
\v 25 Yahweh mai runduna zai albarkace su ya ce, "Mai albarka ce Masar, jama'ata; Asiriya, aikin hannuwana; da Isra'ila, abin gãdona."
\c 20
\cl Sura 20
\p
\v 1 A cikin shekarar da Tartan ya zo Ashdod, sa'ad da Sargon sarkin Asiriya ya aiko shi, ya yi faɗa gãba da Ashdod ya amshe ta.
\v 2 A wannan lokaci Yahweh ya yi magana ta wurin Ishaya ɗan Amoz yace, "Ka je ka tuɓe tsummokara daga ƙugunka, ka tuɓe takalma daga ƙafafunka." Ya yi haka, ya yi tafiya huntu ba takalma a ƙafafunsa.
\v 3 Yahweh yace, "Kamar yadda bawana Ishaya ya yi tafiya huntu ba takalma a ƙafafunsa shekara uku, wannan alama ce da al'ajibi dangane da Masar da Kush -
\v 4 ta haka sarkin Asiriya zai tafi da kamammu na Masar, da korarru na Kush, tsoho da yaro, huntu ba takalmi, da ɗuwawunsu a waje, domin Masar ta kunyata.
\v 5 Za su karaya su ji kunya, saboda Kush begensu da Masar darajarsu.
\v 6 Mazaunan wannan yanki a cikin wannan rana za su ce, 'Hakika, wannan shi ne tushen begenmu, inda mu kan ruga neman taimako domin a cece mu daga sarkin Asiriya, to yanzu, ta yaya za mu tsira?"'
\c 21
\cl Sura 21
\p
\v 1 Furci game da hamada ta wajan teku. Kamar guguwa mai sharewa ta bi ta Negeb, ta zo tana wucewa ta cikin jeji, daga ƙasa mai ban tsoro.
\v 2 An ba ni ruya mai ban razana: mutum marar imani yana yin rashin imani, mai hallakarwa yana hallakarwa. Jeka ka kai hari, a kan Ilam; yi sansani, Midiya; zan tsaida dukkan rurinta.
\v 3 Saboda haka kwankwasona ya cika da ciwo; ciwo kamar irin ciwon mace mai naƙuda ya kama ni; abin da na ji ya durƙusar da ni; abin da na gani ya tada hankalina.
\v 9 Ga karusa tana zuwa da mutum da tagwayen mahaya. Ya yi kira, "Babila ta faɗi, ta faɗi, dukkan sassaƙaƙƙun siffofin allolinta kuma sun ragargaje har ƙasa."
\v 16 Gama abin da Yahweh ya faɗa mani ke nan, "A cikin shekara ɗaya, kamar yadda ma'aikacin da a ka ɗauka domin shekara ɗaya zai gani, dukkan darajar Keda za ta ƙare.
\v 17 Maharba kaɗan kawai, da jarumawan Keda 'yan kaɗan za su rage," gama Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗi.
\c 22
\cl Sura 22
\p
\v 1 Furci game da Kwarin Wahayi: Mene ne dalilin da ya kai dukkan ku bisan gidaje?
\v 5 Gama akwai ranar hargitsi, tana tattakowa, da ruɗami domin Ubangiji Yahweh mai runduna, a Kwari na Wahayi, da rushewar ganuwoyi, da mutane suna kuka ga duwatsu.
\v 13 Amma duba, maimakon haka, sai buki da annashuwa, da yanka shanu da tumaki, da cin nama da shaye-shayen ruwan inabi; bari mu ci mu sha, gama gobe za mu mutu.
\v 14 An bayyana mani haka a kunnuwana daga wurin Yahweh mai runduna: "Babu shakka ba za a gafarta maku wannan muguntar ba, ko kun mutu," inji Ubangiji Yahweh mai runduna.
\v 16 "Me ka ke yi a nan, wane ne ya ba ka izini ka gina kabari domin kanka, sassaƙa kabari ya ke yi a wurare masu tsawo, yana sassaƙawa kansa wurin hutawa a cikin dutse?"'
\v 18 Ba shakka zai yi majaujawa da kai, kamar ƙwallo zai wurga ka a cikin ƙasa mai girma. Can za ka mutu, can kuma karusanka masu daraja za su kasance; za ka zama abin kunyar gidan shugabanka!
\v 20 Zai zama a wannan rana zan kira bawana Iliyakim ɗan Hilkiya.
\v 21 Zan tufasantar da shi da alkyabbarka in ɗaura masa ɗamararka, zan maida muƙaminka a hannunsa. Za ya zama uba ga mazaunan Yerusalem da gidan Yahuda.
\v 22 Zan ɗora mabuɗin gidan Dauda a kafaɗarsa; zai buɗe, kuma ba mai kullewa; zai kulle, kuma ba mai buɗewa.
\v 23 Zan kafa shi, kamar ƙusa a wuri mai tsaro, zai zama mazaunin ɗaukaka domin gidan ubansa.
\v 24 Za su rataya masa dukkan ɗaukakar gidan ubansa, 'ya'ya da zuriya-zuriya, kowanne ƙaramin wurin ajiya daga ƙoƙuna zuwa dukkan moɗaye.
\v 25 A wannan rana - wannan furcin Yahweh mai runduna ne - ƙusar da a ka kafa a wuri mai ƙarfi za ta cire, ta karye, ta kuma faɗi, nauyin dake kanta kuma zai yanke - Gama Yahweh ya furta.
\c 23
\cl Sura 23
\p
\v 1 Furci game da Taya: Ku yi ruri, ku jiragen Tarshish; domin babu gida ko wurin tsayawa; daga ƙasar Sifuros an bayyana masu.
\v 4 Ki ji kunya, ke Sidon; gama teku ya yi magana, babba na teku. Ya ce, "Ban yi naƙuda ba ban haihu ba, ban yi renon samari ba, ban tarbiyantar da 'yammata ba."
\v 7 Wannan ya faru da ku ne, birni mai farinciki, wanda tushenta tun daga zamanin dã ne, wadda ƙafafunta sun kai ta can nesa zuwa bãƙin wurare ta zauna?
\v 12 Ya ce, "Ba za ki ƙara yin farinciki ba, ke mai shan tsanani ɗiyar budurwa ta Sidon; ki tashi, ki wuce zuwa Sifuros; Amma ko can ma ba za ki sami hutu ba."
\v 13 Dubi ƙasar Kaldiyawa. Waɗannan mutane yanzu ba su; Asiriyawa sun maida ita daji domin dabbobin jeji. Sun kafa hasumiyoyin sansaninsu; sun rushe fãdojinta; sun maida ita tsibin kufai.
\v 15 A wannan rana, za a manta da Taya har shekara saba'in, kamar kwanakin sarki. Bayan shekara saba'in ɗin wani abu zai faru da Taya kamar yadda ya ke a cikin waƙar karuwa.
\v 17 Zai zama bayan shekara saba'in, Yahweh zai taimaki Taya, za ta fara samun kuɗi ta wurin aikin karuwanci, za ta bada hidimarta ga dukkan mulkokin duniya.
\v 18 Ribarta da abin da take samu za a keɓe shi ga Yahweh. Ba za a tara su ko a ajiye su a ma'aji ba, gama za a bada ribarta ga waɗanda suke zama a gaban Yahweh domin ayi amfani da su a ba su abinci isashshe saboda su sami tufafi mafi daraja.
\c 24
\cl Sura 24
\p
\v 1 Duba, Yahweh ya kusa mayar da duniya kango, ya lalata ta, ya ɓata fuskarta, ya watsar da mazauna cikinta.
\v 2 Za ya zama cewa, kamar yadda ya ke da mutane, haka kuma firist; kamar yadda iyayengiji suke haka bayi za su zama, kamar yadda uwargijiya take, haka kuyangarta za ta zama, kamar yadda mai sayarwa ya ke, haka mai saye za ya zama; kamar yadda mai bada bashi ya ke, haka mai karɓar bashin za ya zama; kamar yadda mai karɓar bashi da ruwa ya ke, haka mai bada wa da ruwa.
\v 16 Mun ji waƙoƙi daga wuri mafi nisa na duniya, "Ɗaukaka ga mai tsarki!" Amma na ce, "Kaito na, na lalace, na lalace! Mazambata sun yi zamba; i, mazambata sun yi zamba ƙwarai."
\v 18 Shi wanda ya gudu saboda jin ƙarar razana zai faɗa rami, kuma shi wanda ya fito daga tsakiyar rami tarko zai kama shi. Tagogin sama za su buɗe, tussan duniya kuma za su girgiza.
\v 23 Sa'an nan rana zata ƙasƙanta wata kuma ya ji kunya, gama Yahweh zai yi mulki a Tsaunin Sihiyona da cikin Yerusalem a gaban dattawansa cikin daraja.
\c 25
\cl Sura 25
\p
\v 1 Yahweh, kai ne Allahna; zan ɗaukaka ka, zan yabi sunanka; saboda ka yi abubuwan ban mamaki, abubuwan da a ka shirya tun dã, cikin cikakken aminci.
\v 4 Gama ka zama mafaka ga wanda ya ke matalauci, mafaka ga fakirai mabuƙata - wurin fakewa daga hadari, wurin fakewa daga zafin rana. Sa'ad da hucin marasa hankali ya ke kamar haɗari mai buga bango,
\v 6 A kan wannan tsaunin Yahweh mai runduna zai yiwa dukkan mutane liyafa da abubuwa masu ƙiba, zaɓaɓen ruwan inabi, da nama mai taushi, liyafar ruwan 'ya'yan itace.
\v 9 A wannan rana za a ce, "Duba, wannan shi ne Allahnmu, mun jira shi, shi kuma zai cece mu. Wannan shi ne Yahweh, mun jira shi, za mu yi murna da farinciki cikin cetonsa."
\v 9 Na ji marmarinka cikin dare; i, ruhuna a cikina ya neme ka da gaske. Gama sa'ad da hukucinka ya zo duniya, mazaunan duniya suna koyo game da adalci.
\v 10 Bari a nuna wa mai mugunta tagomashi, amma ba zai koyi adalci ba. A cikin ƙasar masu tafiya dai-dai, shi mugunta ya ke yi kuma darajar Yahweh shi bai san ta ba.
\v 11 Yahweh, an tada hannunka sama, amma su ba su lura ba, amma za su ga himmar ka domin mutane za su ji kunya, saboda wutar magabtanka za ta cinye su.
\v 17 Kamar mace mai juna biyu sa'ad da lokacin haihuwar ta ya yi kusa, tana zafin ciwon naƙuda ta kuma yi kuka gare ka, haka muke a gaban ka, Ubangiji.
\v 19 Matattun ka za su rayu; jukkunan su da suka mutu za su tashi. Ku farka ku raira waƙar farinciki, ku mazauna cikin ƙura; gama raɓarku raɓar haske ce, ƙasa kuma za ta fito da matattunta.
\v 21 Gama, duba, Yahweh ya kusa fitowa daga wurinsa ya hori mazaunan duniya saboda muguntarsu; ƙasa za ta buɗe zubar da jinin da ta yi, ba zata ƙara ɓoye waɗanda ta kashe ba.
\c 27
\cl Sura 27
\p
\v 1 A wannan rana Yahweh zai hori Lebiyatan macijin nan mai gudu da takobinsa mai girma, mai karfi, mai ban tsoro, Lebiyatan macijin nan mai tafiya a shagide, zai kashe babban dodon ruwa dake cikin teku.
\v 7 Yahweh, ya kaiwa Yakubu da Isra'ila hari kamar yadda ya kaiwa al'umman da suka kai masu hari? An kashe Yakubu da Isra'ila kamar yadda aka kashe al'umman da suka kashe su?
\v 8 Ka yi fama bisa mizanin da ya yi dai-dai, ka sallami Yakubu da Isra'ila suka tafi; ka kore su da iska mai ƙarfi sun tafi, a wannan rana ta iskar gabas.
\v 9 Haka a wannan rana, za a rufe muguntar Yakubu, wannan shi ne cikakken 'ya'yan kawar da zunubi: sa'ad da zai farfasa duwatsun bagadi ya yi masu gutsu-gutsu kamar alli, ba za a sami sifofin Asheran ko bagadin turarenta a tsaye ba.
\v 11 Sa'ad da ƙiraruwan suka bushe, za a kakkarye su. Mataye za su hura wuta da su, gama mutane ne marasa fahimta. Wanda ya yi su ba za ya ji tausayin su ba, shi wanda ya yi su ba za ya nuna masu jinƙai ba.
\v 12 Rana zata zo inda Yahweh zai yi shiƙa tun daga Kogin Yuferitis har zuwa Wadi ta ƙasar Masar, ku kuma mutanen Isra'ila za a tattaro ku ɗai-ɗai da ɗai-ɗai.
\v 13 A wannan rana za a busa babban ƙaho; lalatattu na ƙasar Asiriya za su zo, da yasassu na ƙasar Masar, cikin Isra'ila za su yi sujada ga Yahweh a kan tsauni mai tsarki cikin Yerusalem.
\c 28
\cl Sura 28
\p
\v 1 Kaiton rawanin girman kai na fure da kowanne mashayan Ifraim ke sanye da shi, kyaun darajarsu na dushewa kamar yadda kyaun fure ke dushewa, haka ma rawanin dake kan waɗanda suka bugu da ruwan inabi a Kwari mai tãki, inda ruwan inabi ya rinjayi wasu!
\v 2 Duba, Ubangiji yana aiko da wani babba, kuma ƙaƙƙarfa; kamar hadari mai ƙanƙara, da iska mai lalatarwa, kamar ruwan sama mai kwararowa da ambaliyar ruwaye; zai jefar da kowanne rawanin fure a ƙasa.
\v 4 Furen ɗaukakarsa mai ƙyau, dake kan kwari mai arziki, zai zama kamar nunannen ɓaure na fãri da damuna, zai zamana, sa'ad da wani ya dube shi, tun yana hannunsa, zai haɗiye su.
\v 7 Amma har ma waɗannan suna tangaɗi da ruwan inabi mai ƙarfi. Da firist da annabi suna tangaɗi da ruwa mai ƙarfi, ruwan inabi ya haɗiye su. Suna tangaɗi da ruwan inabi mai ƙarfi, suna tangaɗi a wahayi da rashin sanin abin yi.
\v 13 Haka maganar Yahweh za ta zama ma su doka bisa doka, doka bisa doka; ka'ida bisa ka'ida, ka'ida bisa ka'ida; nan ɗan kaɗan, can ɗan kaɗan; domin su tafi da baya su faɗi, a karya su, a sa masu tarko, a kama.
\v 15 Wannan zai faru domin kun ce, "Mun yi alƙawari da mutuwa, da muka ƙulla yarjejeniya. Saboda haka lokacin da babbar bulala mai bin kan kowa zata ratsa, ba zai iso wurin mu ba. Gama mun mai da ƙarya mafaƙarmu, mun sami mafaka a rumfa cikin ƙarya."
\v 16 Saboda haka Ubangiji Yahweh yace, "Duba: Zan kafa harsashin dutse a Sihiyona, dutsen da aka jaraba, dutsen kusurwa mai daraja, tabbataccen harsashi, duk wanda ya gaskata ba za ya kunyata ba.
\v 19 Duk lokacin da za su wuce, za su sha kanku, daga safiya zuwa safiya za su yi ta aukowa, kuma dare da rana za su wuce kuma da rana da dare zai zo. Sa'ad da aka fahimci saƙon, zai sa firgita.
\v 21 Yahweh zai miƙe kamar a kan Dutsen Ferazim, zai tashi kansa kamar a cikin Kwarin Gibiyan domin ya yi aikinsa, bãƙon aikinsa, ya kuma yi bãƙon aikinsa.
\v 25 Lokacin da ya shirya ƙasar, ba yakan yafa tamba ba, ya warwatsa riɗi, sai ya sa alkama a jere, da bali a inda ya kamata, da kuma wasu irin a gefuffuka?
\v 27 Bugu da ƙari 'ya'yan tamba ba a sussukasu da haƙoran ƙarfe, ba a kuma bin kan riɗi da tayar karusa; amma akan buga tamba da 'gora, riɗi kuma da sanda.
\v 4 Za a jawo ki ƙasa za ki yi magana daga ƙasa; muryarki zata dushe a cikin ƙura. Muryar ki zata zama kamar ta ruhu dake fitowa daga ƙasa, maganar ki kuma zata zama rarrauna daga cikin ƙura.
\v 6 Yahweh mai runduna zai zo maki, da tsawa, da raurawar ƙasa, da ƙara mai tsanani, da babbar iska, da gawurtaccen hadari, da harshen wuta mai hallakarwa,
\v 7 Zai zama kamar mafarki, wahayi da dare: Taron dukkan al'ummai za su yaƙi Ariyel da kagararta. Za su hare ta da ita da garunta domin su matsa mata.
\v 8 Zai zama kamar lokacin da mayunwacin mutum ya ke mafarki yana cin abinci, amma da ya farka, cikininsa ba komai. Zai zama kamar lokacin da wani mutum yana jin kishin ruwa, sai ya yi mafarki yana shan ruwa, amma lokacin da ya farka, yana suma, kishin ruwansa ba a kashe ba. I, haka zai zama ga dukkan al'umman da za su yaƙi Dutsen Sihiyona.
\v 11 Dukkan wahayi ya zamar maku kamar maganganun littafin da a ka kulle, wanda mutane za su ba masani, su ce, "Karanta wannan." Shi kuma zai ce, "Ba zan iya ba gama an kulle."
\v 13 Ubangiji yace, "Waɗannnan mutane suna kusatowa gare ni da bakunansu, suna kuma girmamani da leɓunansu, amma zuciyarsu tana nesa da ni. Girman da suke ba ni na dokokin mutane ne da a ka riga a ka koya.
\v 14 Saboda haka, duba, zan ci gaba in yi abin ban mamaki cikin mutanen nan, al'ajibi kan al'ajibi. Hikimar masanansu zata lalace kuma fahimtar masu tattalinsu zasu ɓace."
\v 16 Kuna juya abubuwa na sama zuwa ƙasa! Za a kwatanta mai ginin tukwane kamar yumɓu, har da abin da a ka yi zai ce game da wanda ya yi shi, "Ba shi ya yi ni ba," ko abin da a ka sarrafa ya cewa wanda ya sarrafa shi, "Bai fahimta ba"?
\v 21 waɗanda ta wurin magana su kan maida mutum mai laifi. Suna kafa tarko ga mai neman a yi mashi adalci a ƙofa su kuma kãda mai adalci da holoƙan ƙarairayi.
\v 22 Saboda haka ga abin da Yahweh ya faɗi game da gidan Yakubu - Yahweh wanda ya fanshi Ibrahim, "Yakubu ba zai ƙara jin kunya ba, ko kuma fuskarsa ta turɓune.
\v 23 Amma sa'ad da zai dubi 'ya'yansa, aikin hannuwana, za su tsarkake sunana. Za su tsarkake sunan Mai Tsarki na Yakubu za su kafu cikin tsoron Allah na Isra'ila.
\v 24 Waɗanda suka ɓata cikin ruhaniya za su sami fahimta, masu gunaguni za su koyi ilimi."
\c 30
\cl Sura 30
\p
\v 1 "Kaiton 'ya'yan tawaye," wannan ne furcin Yahweh. Suna shirye-shirye, amma ba daga gare ni ba; suna ƙulla yarjejeniya da wasu al'ummai, amma ba Ruhuna ya bishe su ba, saboda haka suna ƙara zunubi kan zunubi.
\v 5 Dukkansu za su ji kunya domin mutanen da ba za su iya taimakonsu ba, waɗanda ba taimako ba ne ko tallafawa, amma abin kunya ne, har ma abin ƙasƙanci."
\v 6 Furci game da dabbobin Negeb: Cikin ƙasar wahala da hatsari, da zakanya da kuma zaki, da kububuwa da miciji mai dafi yana shawagi, su kan labta arzikinsu bisa jakkai, da kayayyakinsu masu daraja bisa doron raƙuma, su kaiwa mutanen da ba za su iya taimaka masu ba. Gama taimakon
\v 14 Zai fasa shi kamar yadda tukunyar magini ke farfashewa; ba zai ƙyale ta ba, don kada a sami cikin farfasassun koda ɗan kaskon da za a ɗauko ɗan garwashin wuta daga sauran garwashin, ko a kwarfo ruwa daga cikin randa.
\v 15 Gama wannan shi ne Ubangiji Yahweh, Mai Tsarki na Isra'ila yace, "Cikin komowa da hutu za ku tsira; cikin natsuwa da dogara ƙarfin ku zai tabbata. Amma ba ku yarda ba,
\v 17 Dubu za su gudu a tsoratawar mutum ɗaya; a tsoratawar biyar za ku gudu har sai sauranku da suka rage sun zama kamar sandar tuta a kan tsauni, ko kamar 'yar tuta a kan tudu."
\v 18 Duk da haka Yahweh yana jira ya yi maku alheri, saboda haka a shirye ya ke ya nuna maku jinƙai. Gama Yahweh Allah ne mai adalci; masu albarka ne dukkan waɗanda suke jiransa.
\v 19 Gama waɗansu mutane za su zauna a cikin Sihiyona, cikinYerusalem, ba za su ƙara yin kuka kuma ba. Hakika zai yi maku alheri da ya ji ƙarar kukan ku. Idan ya ji shi, zai amsa maku.
\v 20 Koda shike Yahweh yana ba ku gurasar wahala da ruwan matsaloli, haka kuma, malaminku ba zai ƙara ɓoye kansa ba, amma za ku ga malamin ku da idanunku.
\v 21 Kunnuwan ku za su ji magana a bayan ku, cewa, "Wannan ita ce hanya, yi tafiya a cikinta," sa'ad da kuka juya zuwa dama ko kuka juya zuwa hagu.
\v 22 Za ku tozartar da sassaƙaƙƙun siffofin ku da a ka dalaye da azurfa da kuma sarrafaffun siffofinku na zinariya. Za ku zubar da su kamar ƙazamtattun tsunmokaran al'ada. Za ku ce masu, "Ku fita daga nan."
\v 23 Zai bada ruwan sama domin iri lokacin da kuka yi shuka a ƙasa, da gurasa tare da yalwa daga ƙasa, amfani kuma zai zama da yawa. A ranar nan shanunku za su yi kiwo a makiyaya mai fãɗi.
\v 24 Shanun noma da jakkai, da suke huɗa, za su ci gyararren abinci wanda aka sheƙe da cebur da matankaɗi.
\v 25 Bisa kowanne dogon tsauni, da bisa kowanne dogon tudu, za a sami maɓuɓɓugai da rafuka masu gudanar da ruwa, a ranar gawurtaccen kisa sa'ad da hasumiyoyi za su faɗi.
\v 26 Hasken wata zai zama kamar hasken rana, hasken rana zai ninka sau bakwai, kamar hasken kwana bakwai. Yahweh zai ɗaure karayar mutanensa ya warkar da ƙujewar raunin da ya yi masu.
\v 27 Duba, sunan Yahweh ya zo daga wuri mai nisa, yana ƙũna da fushinsa kuma a cikin turmuƙin hayaƙi. Leɓunansa suna cike da zafi, harshensa kuma na kama da wuta mai cinyewa.
\v 28 Numfashinsa yana kama da ambaliya wanda ruwansa ya kai har tsakiyar wuya, domin ya rairaye al'ummai da matankaɗin hallakarwa. Numfashinsa linzami ne a muƙamuƙan mutane yasa su warwatse.
\v 29 Za ku sami waƙa da dare sa'ad da kuke biki mai tsarki, da murna a zuciya, kamar yadda wani zai tafi da sarewa bisa tsaunin Yahweh, zuwa ga Dutsen Isra'ila.
\v 33 Domin an shirya wurin ƙũna tuntuni. Hakika, an shirya shi domin sarki, Allah ya shirya shi da zurfi da kuma faɗi. Tarin kuwa a shirye ne da wuta da kuma itace da yawa. Numfashin Yahweh, kamar rafin ƙibiritu ne da zai cinna masa wuta.
\c 31
\cl Sura 31
\p
\v 1 Kaiton waɗanda suke gangarawa zuwa Masar domin neman gudummuwa suna jingina ga dawakai, suna dogara ga karusai, (domin suna da yawa), da kuma mahayan dawakai (domin sun zarce ƙididdiga). Amma ba su damu da Mai Tsarki na Isra'ila ba, ba su kuma neman Yahweh!
\v 2 Duk da haka yana da hikima, zai kuwa kawo masifa ba zai janye maganarsa ba. Zai tashi gãba da gidan mugunta, gãba kuma da kai gudummuwa ga masu aikata zunubi.
\v 3 Masar mutum ne ba Allah ba, dawakansu kuma jiki ne ba ruhu ba. Lokacin da Yahweh zai miƙar da hannunsa, dukka da wanda ya yi gudummuwar zai yi tuntuɓe, wanda kuma a ka yiwa gudummuwar zai faɗi; su biyun za su hallaka tare.
\v 4 Ga abin da Yahweh yace mani, "Kamar yadda zaki, har ma ɗan zaki ya kan yi ruri a kan dabbar da ya kashe, sa'ad da a ka kira ƙungiyar makiyaya a kansa, amma ba ya rawar jiki saboda muryoyinsu, ko ya sulale domin ƙararsu; haka Yahweh mai runduna zai sauko ya yi yaƙi a kan Dutsen Sihiyona, a kan tudun nan.
\v 5 Kamar tsuntsaye masu shawagi bisa sheƙarsu, haka Yahweh mai runduna zai tsare Yerusalem; zai tsare ya kuma cece ta sa'ad da ya ke wuce wa bisanta ya kare ta.
\v 9 Za su karai saboda razana, sarakunansu za su tsorata idan sun ga tutar yaƙin Yahweh - wannan furcin Yahweh ne - wanda wutarsa ke cikin Sihiyona, tanderun wutarsa kuma tana cikin Yerusalem.
\c 32
\cl Sura 32
\p
\v 1 Duba, wani sarki zai yi sarauta cikin adalci, yarimai kuma za su yi mulki da gaskiya.
\v 6 Domin wawa yakan faɗi wauta, zuciyarsa takan shirya mugunta da mugayen ayyuka, yana kuma faɗar ƙarya akan Yahweh. Yakan tsiyatar da mayunwata, masu jin ƙishirwa kuma ya sa su rasa abin sha.
\v 7 Dabarun mayaudari mugaye ne. Yakan ƙago mugayen shirye-shirye, domin ya lalatar da matalauta da ƙarairayinsa, koda matalaucin ya faɗi abin dake dai-dai.
\v 10 Gama nan gaba kaɗan da shekara guda ƙarfin halinku za a karya, ku mata masu zaman sake, gama ba za a sami girbin inabi ba, kuma ba amfanin da za a tattara a rumbuna.
\v 11 Ku yi rawar jiki don tsoro, ku mata masu zaman sake; ku yi damuwa, ku masu ƙarfin hali; ku tuɓe ƙyawawan tufafinku, ku tsirance kanku; ku ɗaura tsummokin makoki a kwankwasonku.
\v 14 Gama za a yasar da fãda, birnin mai cincirindon mutane zai koma kango; da tudu da benen tsaro za su zama kogonni har abada, abin murna ga jakan jeji, wurin kiwo domin garkuna;
\v 20 ku da kuka yi shuka a bakin rafuffuka za a albarkace ku, da dukkan ku da kuke aika shanunku da jakai su yi kiwo.
\c 33
\cl Sura 33
\p
\v 1 Kaiton ka, mai ɓatawa ba a ɓata ka ba! Kaiton ka mai cin amanar waɗanda ba su ci amanarka ba! Lokacin da ka bar ɓatawa, za a ɓata ka. Lokacin da ka daina cin amana, za a ci amanar ka.
\v 9 Ƙasar tana makoki, duk ta yi yaushi; Lebanon ta kunyata ta kuma yi yaushi; Sharon kamar ƙasar filin hamada take; Bashan kuma da Kamel sun kakkaɓe ganyayensu.
\v 14 Masu zunubi a Sihiyona sun tsorata; makyarkyata ta kama marasa tsoron Allah. Wane ne a cikin mu zai iya zama da wuta mai ruruwa? Wane ne a cikin mu zai iya zaunawa da madawwamin ƙone-ƙone?
\v 15 Shi wanda ya ke tafiya bisa adalci yana magana da gaskiya; wanda ke ƙin ribar zilama, yana ƙin karɓar toshi, ba ya shirye-shiryen ta'addanci; ba ya duban mugunta -
\v 20 Dubi Sihiyona, birnin bukukuwanmu; idanunku za su ga Yerusalem kamar mazauni mai lafiya, rumfar da ba za a kawas ba, ƙusoshin ta ba za a tumbuƙe su ba, kuma igiyoyinta ba za a katse su ba.
\v 21 Maimakon haka, Yahweh cikin daraja zai kasance tare damu, a wuri mai manyan koguna da rafuffuka. Ba jirgin ruwan yaƙi da zai bi ta cikinsa, ba kuma manyan jiragen da za su bi ta wurin.
\v 23 An kwance maɗaurinka, ba za su iya riƙe tirken tutar jirgin ruwa da ƙarfi ba; ba za su iya baza tutar jirgin ruwa ba; sa'ad da za a raba babbar ganima, har gurgu ma zai sami rabo.
\v 24 Mazaunan wurin ba za su ce, "Ba ni da lafiya ba," mutanen dake zaune a can za a gafarta zunubansu.
\c 34
\cl Sura 34
\p
\v 1 Ku matso kusa, ku al'ummai, ku saurara; ku natsu, ku mutane! Duniya da dukkan cikarta dole su saurara, duniya, da dukkan abin da ke fitowa a cikinta.
\v 4 Dukkan taurarin sama za su dushe, za a naɗe sammai kamar naɗaɗɗen littafi; dukkan taurarinsu za su dushe, kamar yadda ganyayen inabi suke karkaɗewa su faɗi daga itacen, kuma kamar yadda nunannun ɓaure ke faɗuwa daga jikin itacensa.
\v 6 Takobin Yahweh na ɗiɗɗigar da jini da kitse, tana ɗiɗɗigar da jinin 'yan raguna da na awaki, rufe da kitsen ƙodojin raguna. Gama Yahweh yana da hadaya a Bozra da kuma babban yanka a ƙasar Idom.
\v 10 Zata ci wuta dare da rana; hayaƙinta zai tashi sama har abada; daga tsara zuwa tsara zata zama yasasshiyar ƙasa; ba wanda zai ratsa ta tsakiyarta har abada abadin.
\v 11 Tsuntsaye jeji da dabbobi za su zauna a wurin; mujiya da hankaka za su yi sheƙar su a cikin ta. Kamar yadda mai gini ya ke amfani da igiyar gwaji haka zai auna ƙasar domin rusarwa da hallakarwa.
\v 14 Dabbobin jeji da kuraye za su tattaru a can, awakan jeji za su kira junansu da kuka. Dabbobin jeji masu yawon dare za su tare a nan su kuma samar wa kansu wurin hutawa.
\v 15 Mujiyoyi za su yi sheƙa, za su nasa ƙwayayensu su ƙyanƙyashe, su ƙyanƙyashe su kuma tsare 'yan ƙananansu. I, a can hankaki za su taru, kowanensu da abokin tarayyarsa.
\v 16 Ku binciko daga naɗaɗɗen littafin Yahweh; ba ko ɗayansu da za a rasa. Ba wanda zai rasa ɗan'uwan tarayyarsa; gama bakinsa ya umarta shi, ruhunsa kuma ya tattara su.
\v 2 zata faso da furanni ainun ta yi murna da farin ciki da waƙa; za a ba shi darajar Lebanon, da kuma ɗaukakar Karmel da Sharon; za su ga ɗaukakar Yahweh, mafificiyar ɗaukakar Allahnmu.
\v 7 Yashi mai ƙuna zai zama tafki, ƙasa mai ƙishin ruwa kuma zata zama maɓuɓɓugar ruwa; a mazaunin diloli, inda dă suka kwanta, za a tarar da ciyawa da iwa.
\v 8 Wata karafka zata kasance a wurin ana kiran ta Hanya Mai Tsarki. Marar tsarki ba zai bi ta kanta ba. Amma zata kasance domin wanda ya yi tafiya a cikinta. Ba wawan da zai bi ta kanta.
\v 10 Baratattun Yahweh za su komo za su taho suna waƙa zuwa Sihiyona, madawwamin farinciki zai kasance a kansu; murna da farinciki za su mamaye su; baƙinciki da ajiyar zuciya za su shuɗe.
\c 36
\cl Sura 36
\p
\v 1 A shekara ta goma sha huɗu ta sarki Hezekiya, Senakerib sarkin Asiriya, ya tasar wa dukkan biranen Yahuda da kagararsu ya kuma kame su.
\v 2 Sai sarkin Asiriya ya aika da babban shugaban soja daga Lakish zuwa Yerusalem ga sarki Hezekiya tare da babban soja. Ya gabaci dai-dai magudanar kwarin da ya ke kawo ruwa, a babbar hanyar filin da masu wankin tufafi suka tsaya a kanta.
\v 3 Shugabannin Isra'ilawa waɗanda suka fito wajen birnin su yi magana da su su ne Hilkiya ɗan Iliyakim, shugaba mai kula da fãda, Shebna sakataren sarki, da Yowa ɗan Asaf, wanda ke rubuta matakan gwamnati.
\v 4 Sai shugaban sojoji yace da su, "Ku faɗawa Hezekiya babban sarki, sarkin Asiriya, yace, 'Me kake dogara da shi?
\v 5 Ka na maganganun wofi marar amfani, cewa akwai shawara da ƙarfin yaƙi. To yanzu ga wa kake dogara? Wane ne ya baka ƙarfin zuciya da za ka yi mani tawaye?
\v 6 Duba, kana dogora da Masar, da tsabgar da kake amfani da ita a matsayin sandar tafiya, amma duk mutumin da ya dogara da ita, zai karye ya soke hannunsa. Wannan shi ne Fir'auna sarkin Masar zai yiwa dukkan wanda ya dogara gare shi.
\v 7 Amma idan ka ce da ni, "Mu na dogara ga Yahweh Allahnmu," ba shi ne wanda ya ke a manyan wurare da bagadai Hezekiya ya ɗauke, ya kuma ce Yahuda da Yerusalem, '"Dole ku yi sujada a wannan bagadi a Yerusalem ba"?
\v 8 Saboda haka yanzu, zan ba ka abu mai kyau daga maigidana sarkin Asiriya. Zan ba ka dawakai dubu biyu, idan har za ka iya samin masu hawansu.
\v 9 Ya ya zaka iya kaucewa ko ɗaya daga cikin barorin shugabana? Kana sa dogara ga karusai da mahaya dawakai na Masar!
\v 10 To yanzu, na tafi can ba tare da Yahweh ba in tasar wa wannan ƙasar, har in lalatar da ita? Yahweh yace da ni, "Ka faɗawa wannan ƙasar har ka lalatar da ita.'""
\v 11 Sa'an nan Iliyakim ɗan Hilkiya, da Shebna, da Yowa suka ce da babban shugaba, "Ka yi magana da barorinka a cikin harshen Aremiyanci, Aremaik, domin muna gane shi. Kada ka yi magana da mu da harshen Yahuda a kunnuwan mutane waɗanda suke a kan garu."
\v 12 Amma babban kwamanda ya ce, "Babban sarki ya aiko ni ga shugabanku kuma ya faɗi waɗannan maganganu? Ba ya aiko ni ga jama'ar da suke a kan garu ba, waɗanda za su ci kashinsu su kuma sha fitsarinsu tare da ku ba?"
\v 13 Sai shugaban sojoji ya tsaya ya tada murya da ƙarfi a cikin Yahudanci, cewa, "Ku saurari magana daga babban sarki, sarkin Asiriya.
\v 14 Sarki yace, 'Kada ku yarda Hezekiya ya ruɗe ku, shi ba zai iya cetonku ba.
\v 15 Kada kuma ku bari Hezekiya ya saku ku dogara ga Yahweh, cewa, '"Yahweh zai tabbatar da cetonku; wannan birni ba za a bada shi a hannun sarkin Asiriya ba.'"
\v 16 Kada ku saurari Hezekiya, domin wannan shi ne abin da sarkin Asiriya yace: 'Ku nemi salama tare da ni kuma ku fito wuri na. Sai kowannenku ya ci daga cikin 'ya'yan inabin gonarsa, daga kuma itacen ɓaurensa, ya kuma sha ruwa daga rijiyon kansa.
\v 17 Za ku yi wannan har saina zo na ɗauke ku zuwa wata ƙasa mai kama da irin ta ku, ƙasa mai hatsi da sabuwar inabi, ƙasa ta gurasa da kuringar inabi.'
\v 18 Kada ku bar Hezekiya ya ruɗe ku, cewa, 'Yahweh zai kuɓutar da ku.' Ko akwai wasu allolin mutanen da suka cece su daga hannun sarkin Asiriya?
\v 19 Ina allolin Hamat da na Arfad? Ina allolin Sefarwayim? Sun ceci Samariya daga ikona?
\v 20 A cikin dukkan allolin waɗannan ƙasashe, akwai wani da ya ceci ƙasarsa daga ikona, ya ya kuke ganin kamar Yahweh zai ceci Yerusalem daga ikona?
\v 21 Amma mutane suka tsaya tsit ba bu kuma wanda ya maida martani, don umarnin sarki, "Kada ku amsa masa."
\v 22 Sai Iliyakim ɗan Hilkiya, wanda ya ke bisa iyalin, Shebna marubuci, da Yowa ɗan Asaf mai kula da tarihi, suka zo wurin Hezekiya da tufaffinsu a kekkece, kuma suka faɗa masa maganganun da shugaban mayaƙa ya faɗa.
\c 37
\cl Sura 37
\p
\v 1 Ya zamana a lokacin da sarki Hezekiya ya ji abin da suka faɗa, ya kekkece tufafinsa, ya rufe jikinsa da tsummoki, ya kuma shiga gidan Yahweh.
\v 2 Ya aika Iliyakim, mai kula da fada, da Shebna marubucin shari'a, da dattawa firistoci, dukkansu suka rufe jikinsu da tsummoki, zuwa wurin Ishaya ɗan Amoz, annabi.
\v 3 Suka ce da shi, "Hezekiya yace, 'Wannan rana ce ranar wahala da wulaƙanci da kunya, mun zama kamar lokacin da za a haifi yaro, amma uwar ba ta da ƙarfin da zata haifi yaron.
\v 4 Watakila Yahweh Allahnka zai ji maganganun shugaban mayaƙansa, wanda sarkin Asiriya uban gidansa ya aiko domin ya wulaƙanta Allah mai rai, ya kuma tsawata wa maganganu waɗanda Yahweh Allahnka ya ji. Yanzu sai ka yi addu'a domin ringin da har yanzu suna nan.'"
\v 5 Sa'ad da barorin sarki Hezekiya suka zo wurin Ishaya,
\v 6 sai Ishaya yace da su, "Ku faɗawa ubangidanku: 'Yahweh yace, "Kada ku ji tsoron irin maganganun da kuka ji, waɗanda dasu barorin sarkin Asiriya suka wulaƙanta ni.
\v 7 Duba, zan sa ruhu a cikinsa, zai kuma ji jita-jitar da zata sa ya koma ƙasarsa. Zan sa shi ya faɗi ƙasa da takobi a cikin ƙasarsa.'"'
\v 8 Sai shugaban mayaƙan ya koma ya kuma sami sarkin Asiriya yana yaƙi da Libna, domin ya ji sarki ya tafi daga Lakish.
\v 9 Sa'ad da Senakerib ya ji Tirhaka sarkin Kush da Masar sun haɗu domin su yi yaƙi da shi, sai kuma ya aika da manzanni zuwa wurin Hezekiya tare da saƙo:
\v 10 "Ka ce da Hezekiya, sarkin Yahuda, 'Kada ka bari Allahnka wanda kake dogara da shi ya ruɗe ka, cewa, 'Yerusalem ba zata faɗa hannun sarkin Asiriya ba."
\v 11 Ku gani, ku kuma ji abubuwan da sarakunan Asiriya suka yiwa dukkan ƙasashe ta wurin lalata su ga baki ɗaya. Kuna tsammani za ku kuɓuta?
\v 12 Ko allolin al'ummai sun kuɓutar da su, al'umman da ubannina suka lalata akwai Gozan, da Haran, Rezef, da kuma mutanen Iden a Tel-assa?
\v 13 Ina sarkin Hamat, da sarkin Arfad, da sarkin biranen Sefarwayim, da Hena, da kuma Iwwa?'"
\v 14 Hezekiya ya karɓi wannan wasiƙar daga hannun manzannin ya kuma karanta ta. Sai ya shiga gidan Yahweh ya baza ta gabansa.
\v 15 Hezekiya ya yi addu'a ga Yahweh:
\v 16 "Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, kai da ka zauna a sama da kerubim, kai kaɗai ne Allah a kan dukkan mulkokin duniya. Kai ka yi sammai da duniya.
\v 17 Ka juyo da kunnuwanka, Yahweh, ka ji mu. Buɗe idanuwanka, Yahweh, ka gani, ka kuma ji maganar Senakerib, wanda ya aika don ya yi ba'a ga Allah mai rai.
\v 18 I' gaskiya ne, Yahweh, sarakunan Asiriya sun lalata dukkan al'ummai da ƙasashensu.
\v 19 Suka sa allolinsu a cikin wuta, domin su ba alloli ba ne amma ayyukan hannunwan mutane ne, itace da dutse ne kawai.
\v 20 Saboda haka Asiriyawa sun lalata su. Yanzu dai, Yahweh Allahnmu, ka cece mu daga ikonsa, saboda dukkan mulkokin duniya su sani kai kaɗai ne Yahweh."
\v 21 Sai Ishaya ɗan Amoz ya aika da saƙo wurin Hezekiya, cewa, "Yahweh, Allah na Israila yace, 'Domin ka yi addu'a gare ni a kan Senakerib sarkin Asiriya,
\v 22 wannan ita ce maganar da Yahweh ya faɗa a kansa: "Akwai budurwar yariya ta Sihiyona ta rena ka kuma tana yi maka dariyar ba'a; budurwar Yerusalem tana girgiza kanta gare ka.
\v 24 Ta wurin barorinka ka rena Ubangiji ka kuma ce, 'Da yawan karusaina har na kai ƙololuwar duwatsu, zuwa tsayin Lebanon. Zan sare dogayen itatuwan sida dana sifuros zaɓuɓɓu, na kuma kai wurare mafi nisa, na jeji mafi 'ya'ya.
\v 26 Baka ji yadda na ƙudura a yi haka tuntuni kuma na aiwatar tun zamanin ḍã? Yanzu ne nake cikawa. Kana nan ne domin ka mai da birane gagara-shiga zuwa tulin kango.
\v 27 Mazaunan su, masu ƙaramin ƙarfi, sun warwatse da kunya. Sun zama tsire-tsire a gona, ɗanyar ciyawa, ciyawar dake kan rufi ko a fili, kafin iskar gabas.
\v 29 Domin harzuƙar ka ta gãba da ni, kuma don girmankanka ya iso kunnuwana, zan sa ƙugiya a hancinka, linzami na kuma a bakinka; zan komar da kai hanyar da ka biyo."
\v 30 Wannan ita ce zata zama alama domin ka: A wannan shekara zaku ci gyauro, a kuma shekara ta biyu zaku shuka daga abin da ya tsiro daga gauron. Amma a shekara ta uku dole zaku yi shuka ku kuma girɓe shi, ku dasa kuringar inabi ku kuma ci 'ya'yanta.
\v 33 Saboda Yahweh ya faɗi wannan a kan sarkin Asiriya: "Ba zai shiga wannan birnin ba kuma ba zai harba kibiya a nan ba. Ba zai zo gare shi ba tare da garkuwa ko ya kafa sansanin tudu gãba da ita.
\v 36 Sai mala'ikan Yahweh ya fito ya fãɗa wa sansanin Asiriyawa, ya kashe sojoji 185,000. Da mutanen suka tashi da sassafe, sai suka ga jukunan matattu a kwakkwance ko'ina.
\v 37 Senakerib sarkin Asiriya ya ƙyale Isra'ila ya koma gida ya zauna a Nineba.
\v 38 Daga bisani, yayin da ya ke sujada a gidan Nisrok allahnsa, 'ya'yansa Adramelek da Shareza suka kashe shi da takobi. Sai suka tsere zuwa ƙasar Ararat. Isahadon ɗansa ya yi sarauta a matsayinsa.
\c 38
\cl Sura 38
\p
\v 1 A kwanakin da Hezekiya ya ke ciwo har ya kusa mutuwa. Sai Ishaya ɗan Amoz, annabi, ya zo wurinsa, ya ce masa, "Yahweh yace, 'Ka kintsa komai dai-dai a gidanka; gama mutuwa za ka yi, ba za ka rayu ba,'"
\v 2 Sai Hezekiya ya juya ya sa fuskarsa a bango ya yi addu'a ga Yahweh.
\v 3 Ya ce, "Idan ka yarda Yahweh, ka tuna yadda na yi tafiya a gabanka da dukkan zuciyata da aminci, yadda na yi abin da ke dai-dai a idanunka." Sai Hezekiya ya yi kuka da ƙarfi.
\v 4 Sai maganar Yahweh ta zo wurin Ishaya, cewa,
\v 5 "Tafi ka ce da Hezekiya, shugaban mutanena, 'Wannan shi ne abin da Yahweh, Allah na Dauda kakanka, ya ce: Na ji addu'arka, na kuma ga hawayenka. Duba, ina shirin ƙara maka shekaru goma sha biyar nan gaba.
\v 6 Daga nan zan cece ka da wannan birnin daga hannun sarkin Asiriya, kuma zan kãre wannan birni.
\v 7 Wannan zai zama alama a gare ka daga Yahweh, zan yi abin da na alƙawarta.
\v 8 Duba, zan komar da inuwa baya da taki goma na hawan benen Ahaz. Saboda haka inuwa ta koma baya da taki goma a kan hawan benen inda ta yi gaba.
\v 12 An datse raina an kuma tafi da shi daga gare ni kamar rumfar makiyayin tumaki; na naɗe raina kamar gado; kana sare ni daga masaƙa; tsakanin rana da dare zaka ƙarar da raina.
\v 21 Yanzu Ishaya yace, "Bari su ɗauki 'ya'yan ɓaure su cura a kuma sa shi akan marurun, zai kuma warke."
\v 22 Hezekiya kuma ya ce, "Me zai zama alama da yasa zan iya zuwa gidan Yahweh?"
\c 39
\cl Sura 39
\p
\v 1 A wannan lokacin sai Maduk-Baladan ɗan Baladan, sarkin Babila, ya aika da wasiƙu tare da kyauta ga Hezekiya; domin ya ji cewa Hezekiya ya yi ciwo ya kuma sami lafiya.
\v 2 Hezekiya kuwa ya ji daɗin waɗannan abubuwa; har ya kuma nuna wa manzannin ɗakin dukiyarsa - wato su azurfa, da zinariya, da kayan yaji, da mai mai daraja, da daƙin kayayyakinsa na yaƙi, da dukkan abin da ke cikin gidansa. Babu sauran wani abu da ya ke da shi a gidansa, ko cikin dukkan mulkinsa, wanda Hezekiya bai nuna masu ba.
\v 3 Sai Ishaya annabi ya zo wurin sarki Hezekiya ya kuma tambaye shi, "Me waɗannan mutane suka ce da kai? Daga ina suka zo?" Hezekiya yace, "Sun zo wuri na daga ƙasa mai nisa ta Babila."
\v 4 Ishaya ya yi tambaya, "Me suka gani a gidanka?" Hezekiya ya amsa, "Sun ga dukkan abin da ya ke a gidana. Babu wani abu mai daraja da ban nuna masu ba."
\v 5 Sai Ishaya yace da Hezekiya, "Saurari maganar da Yahweh mai runduna:
\v 6 'Duba, ranaku sun kusa zuwa da za a kwashe komai a fadarka, abubuwan da kakaninka suka tara har ya zuwa yau, za a ɗauke su zuwa Babila. Ba abin da za a rage, in ji Yahweh.
\v 7 'Ya'ya da aka haifa maka, waɗanda kai ka haife su - za a ɗauke su, kuma za su zama bãbãnni a fadar sarkin Babila.'"
\v 8 Sai Hezekiya ya cewa Ishaya, "Maganar Yahweh wadda ka faɗa tana da kyau." Domin ya yi tunani, "Za a sami salama da kwanciyar rai a zamanina."
\c 40
\cl Sura 40
\p
\v 1 "Ta'aziya, ta'azanta mutanena," in ji Allahnka.
\v 2 "Yi magana mai taushi ga Yerusalem; ka yi mata shela cewa yaƙinta ya zo ƙarshe, laifofinta kuma an gafarta mata, za ta sami ruɓi biyu daga hannun Yahweh domin dukkan zunubanta."
\v 9 bisa tsauni mai tsayi, Sihiyona, mai ɗauke da labari mai daɗi. Ki yi kuwwa da ƙarfi, yaYerusalem. Ke da kika kawo labari mai daɗi, daga muryarki, kada kuwa ki ji tsoro. Ki faɗa wa biranen Yahuda, "Ga Allahnku!"
\v 10 Duba, Ubangiji Yahweh yana zuwa kamar mayaƙi mai nasara, damtsensa mai ƙarfi zai yi masa mulki. Ga shi, da sakamako tare da shi, kuma waɗanda ya ceto sun sha gabansa.
\v 11 Zai ciyar da garkensa kamar makiyayi, zai tattara 'yan tumakin a damtsensa, ya kuma ɗauke su kusa da zuciyarsa, kuma a hankali zai bida tumaki masu shayar da nono.
\v 12 Wa ya taɓa auna ruwaye da tafin hannunsa, ko ya auna sararin sama da tafin hannunsa, ko ya iya riƙe ƙurar duniya a kwando, ko ya iya auna nauyi tsaunika a sikeli, ko tuddai a ma'auni?
\v 22 Shi wanda ya ke zaune a bisa bangon duniya; mazaunanta suna kama da fãri a gabansa. Ya miƙar da sammai kamar labule kuma ya baza su kamar rumfa domin a zauna ciki.
\v 24 Suna kama da dashe kasafai, dashen da a ka shuka kasafai, dashen da bai yi ko saiwar da ta shiga ƙasa ba, sa'ad da ya hura a kansu sai su yi yaushi, kuma iskar ta hure su kamar ƙaiƙayi.
\v 26 Dubi sararin sama a bisa! Wane ne ya halicce dukkan waɗannan taurarin? Shi ne wanda ya ke masu jagora kuma ya kira su bisa ga sunan kowa. Ta wurin ikonsa da girmansa da kuma ta wurin karfi da iko, ba ko ɗayansu da ya ɓace.
\v 28 Ba ku sani ba? Ba ku kuma ji ba? Madawwamin Allah, Yahweh, shi ne mahaliccin ƙarshen duniya, ba ya taɓa jin gajiya ko kasala ba; ba shi da iyakar fahimta.
\v 31 Amma waɗanda suke dogara ga Yahweh zai sabunta ƙarfinsu; za su tashi da fikafikai kamar gaggafa; za su yi gudu kuma ba za su gaji ba; za su yi tafiya amma ba za su suma ba.
\c 41
\cl Sura 41
\p
\v 1 "Ku yi shiru ku kasa kunne gare ni, ku manisantan ƙasashe; bari ƙasashe su sabunta ƙarfinsu; bari su matso kusa su yi magana; bari mu taru ga yin jayayya a kan saɓanin.
\v 2 Wane ne wannan da ya motso wani daga gabas, ana kiransa cikin adalci ga aikinsa? Ya bada ƙasashe a gare shi ya kuma taimaka masa har ya yi nasara a kan sarakuna. Ya maida su ƙura da takobinsa, kamar ciyawar da iska ta hure da bakansa.
\v 4 Wane ne yasa wannan ya faru kuma su wane ne suka yi waɗannan ayyuka? Wane ne ya kirawo tsararraki tun daga farko? Ni, Yahweh, na farko, da na ƙarshe, Ni ne shi.
\v 7 Masassaki yana ƙarfafa maƙerin zinariya, kuma wanda ya ke aiki da guduma yana ƙarfafa shi wanda ya ke aiki da tubalin ƙarfe, haka nan ya ke cewa mai walda, yana da kyau.' Suna buga ƙusoshi masu ƙarfi domin kada su tuntsure,
\v 10 Kada ka ji tsoro, ina tare da kai. Kada ka damu da komai, ni ne Allahnka. Zan ƙarfafa ka, zan kuma taimake ka, zan tallafe ka da hannunna na dama mai adalci.
\v 15 Duba, zan sa ku zama kamar ceburin sussuka mai kaifi, sabo mai baki biyu; za ku sussuke tsaunuka ku lalatar da su; za ku niƙe tuddai kamar ƙaiƙayi.
\v 17 Waɗanda ake takurawa da mabuƙata za su nemi ruwa, amma ba bu, harsunansu za su bushe da ƙishi; Ni Yahweh, zan amsa addu'arsu; Ni Allah na Isra'ila, ba zan yashe su ba.
\v 18 Zan sa kogunan ruwa su yi gudu daga gangare, maɓuɓɓugan ruwa su yi gudu a tsakiyar kwarurruka; zan sa hamada ta zama kududdufan ruwa, busasshiyar ƙasa kuma ta zama maɓuɓɓugan ruwa.
\v 19 Zan sa itatuwan sida, da gawo su tsiro a jeji, da itacen ci-zaƙi, da itacen zaitun. Zan dasa siferas a hamada, tare da marke da wuraren renon itacen siferas.
\v 22 Bari ku kawo ma na jayayyarku; ku zo ga ba ku furta ma na abin da da zai faru, saboda mu san waɗannan abubuwa sosai. Ku sa su faɗa mana yadda furcin za su zama, domin mu yi tunani a kansu mu kuma san yadda su ka cika.
\v 23 Ku faɗa game da abubuwan da za su faru nan ga ba, domin mu san ko ku alloli ne; ku yi wani abu mai kyau ko bala'i, ko ma cika da jin tsoro ya kuma burgemu.
\v 25 Na ta da wani daga arewa, kuma ya zo; daga fitowar rana na kira shi wanda ya yi kira bisa sunana, wanda zai tattake masu mulki kamar laka, kamar yadda maginin tukwane ya ke tattake yumɓu.
\v 26 Wa ne ne ya faɗa ma na wannan tun daga farko, ko ma sani? Kafin wannan lokaci, ko mu ce, "Ya yi dai-dai"? Babu ɗayansu da ya yi dokar haka, i, ba kuwa wanda ya ji kuna faɗar wani abu.
\v 5 Ga abin da Allah Yahweh ya faɗa - shi wanda ya halicci sammai kuma ya shimfiɗasu, shi wanda ya yi duniya da dukkan abin da take fitarwa, shi wanda ya ke bayar da numfashi ga mutanen dake cikin ta da kuma rai ga waɗanda ke zaune a cikin ta:
\v 10 Ku raira sabuwar waƙa ga Yahweh, da kuma yabonsa daga ƙarshen duniya; ku waɗanda ke gangarawa zuwa teku, da dukkan abin da ke ciki, ƙasashen tsibirai da dukkan mazaunan cikin su.
\v 11 Bari hamada da biranenta su koka, ƙauyuka kuma inda keda ke zaune, ku yi sowa ta farinciki! bari mazauna Sela su raira; bari su yi sowa daga ƙololuwar tsaunuka.
\v 13 Yahweh za ya fita a matsayin mayaƙi; a matsayin mutumin yaƙi za ya motsa himmarsa. Za ya yi sowa, I, za ya yi kururuwar koke-koken yaƙinsa; za ya nuna wa maƙiyansa ikonsa.
\v 16 Zan kawo makafi bisa hanyar da ba su sani ba; bisa tafarkun da ba su san zan bi da su ba. Zan mayarda duhu ya zama haske a gabansu, zan sa karkatattun wurare su miƙe. Zan yi waɗannan abubuwa, ba kuma zan yashe su ba.
\v 17 Za a komar da su baya, za a san ya su cikin kunya gabaɗaya, wato su waɗanda suka sa dogararsu ga sassaƙaƙƙun siffofi, su waɗanda suke cewa sarrafaffun siffofin ƙarfe, "Ku ne allolinmu."
\v 22 Amma waɗannan mutane ne waɗanda a ka yiwa fashi a ka kuma washe su; an datse su dukka a ramuka, sun zama abin washe wa ba bu kuma mai fansarsu, ba bu wanda kuma ya ce, "A maido da su!"
\v 25 Domin wannan ya zubo da fushinsa mai zafi a bisansu, da masifar yaƙi. Ya haska kewaye da su, amma ba su lura ba; ya ƙona su, amma ba su yi hattara ba a zukatansu.
\c 43
\cl Sura 43
\p
\v 1 Amma yanzu ga abin da Yahweh ya faɗa, shi wanda ya halicceka, Yakubu, shi wanda ya yi ka, Isra'ila: "Kada ka ji tsoro, gama na fansheka; na kiraka da sunanka, kai nawa ne.
\v 2 Sa'ad da ka bi ta cikin ruwaye, zan kasance tare da kai; ta cikin koguna kuma, ba za su sha kanka ba. Sa'ad da ka yi tafiya ta cikin wuta ba za ka ƙone ba, harsashen wutar kuwa ba za ya lalatar da kai ba.
\v 4 Tunda kana da tamani da muhimmanci a idanuna, ina ƙaunarka; saboda haka zan bayar da mutane misanya dominka, wasu mutanen kuma misanya domin rayuwarka.
\v 9 Dukkan al'ummai ku tattaru wuri ɗaya, dukkan mutane kuma ku taru. Wane ne a cikinsu za ya furta wannan, ya kuma yi mana shelar al'amuran farko? Bari su kawo shaidunsu su tabbatar da gaskiyarsu, bari su saurara su kuma tabbatar, 'Gaskiya ne.'
\v 10 Ku ne shaiduna," Yahweh ya furta, "Bawana kuma wanda na zaɓa, domin ku sani ku kuma gaskata da ni, ku kuma fahimci cewa ni ne shi. Kafin ni babu wani allah da a ka yi, kuma ba za ayi wani ba bayana.
\v 14 Wannan ne abin da Yahweh yace, Mai fansarku, Mai tsarki na Isra'ila: "Sabili da ku na yi aike a Babila na turasu dukka zuwa gudun hijira, na maida farincikin Babiloniyawa zuwa waƙoƙin makoki.
\v 17 wanda ya bida karusa da doki, sojoji da babbar runduna. Suka faɗi tare; ba za su sake tashi ba; an kawar da su, aka ɓice su kamar lagwanin da ke ci.)
\v 23 Ba ku kawo mani ko ɗaya daga cikin tumakinku ba a matsayin baye-bayen ƙonawa, ko kuka girmamani da hadayunku ba. Ban ɗora maku nauyin baye-bayen hatsi ba, ko na gajiyar daku da kawo turare.
\v 24 Ba ku sawo mani ƙiraren ƙanshi da kuɗi ba, ko kuwa ku zubo mani kitsen hadayunku ba; amma kuna ɗoramani nauyin zunubanku, kun gajiyar da ni da miyagun ayyukanku.
\v 2 Ga abin da Yahweh yace, shi wanda ya yi ka ya kuma nasa ka cikin mahaifa wanda kuma za ya taimake ka: "Kada ka ji tsoro, bawana Yakubu; da kai kuma, Yeshurun, wanda na zaɓa.
\v 3 Gama zan zubo da ruwa a bisa ƙasa mai ƙishi, da magudanan ruwa a bisa busasshiyar ƙasa; zan zubo da Ruhuna a bisa zuriyarku, da albarkata a bisa 'ya'yanku.
\v 5 Wani za ya ce, 'Ni na Yahweh ne,' wani kuma za ya yi kira ga sunan Yakubu, wani kuma zaya rubuta a kan hannunsa, 'Na Yahweh ne,' ya kuma raɗawa kansa suna da sunan Isra'ila."
\v 6 Wannan ne abin da Yahweh yace - Sarkin Isra'ila da mai fansarsa, Yahweh mai runduna: "Ni ne farko, ni ne kuma ƙarshe; babu kuma wani Allah sai ni.
\v 7 Wane ne kamar ni? bari ya yi shela kuma ya yi mani bayanin al'amuran da suka afku tunda na kafa mutanen dã, bari kuma su yi bayanin al'amuran da za su zo.
\v 8 Kada ku ji tsoro ko ku firgita. Ba na furta maku ba tuntuni, na kuma shelarda shi? Ku ne shaiduna: Akwai wani Allah baya gare ni? Babu wani Dutse; bansan da wani ba."
\v 11 Duba, dukkan abokan tarayyar shi za su sha kunya; masu sassaƙa shi mutane ne kawai. Bari su ɗauki matsayinsu tare; za su noƙe kuma za a sa su sha kunya.
\v 12 Maƙeri na aiki da kayan aikinsa, ya yi su, ya zuga su a garwashi. Ya siffantashi da guduma ya aikatashi da ƙarfin damtsensa. Ya ji yunwa, ƙarfinsa ya ƙare; bai sha ruwa ba sai ya sume.
\v 13 Kafinta yana gwada katako da abin gwaji, za ya yi mashi zane-zane da abin salo. Da kayan aikinsa zai yi masa siffofi, ya zãne shi da abin zãne. zai yi shi siffa-siffa bisa ga siffar mutum, kamar mutum mai ban sha'awa, domin ya zauna a cikin gida.
\v 14 Yana saro itatuwan sida, ko ya zaɓo itatuwan sifares ko itacen rimi. Yana ɗaukowa kansa itatuwa daga jeji. Za ya dasa itacen fir ruwan sama kuma za ya sa ya yi girma.
\v 15 Sai mutum ya yi amfani da shi ya kunna wuta kuma ya ji ɗumi. I, yana kunna wuta ya gargasa gurasa. Daga ciki kuma yana ɗauka ya yi wa kansa allah sai ya rusuna masa; ya yi wa kansa gumaka kuma ya rusuna masa.
\v 16 Daga cikin katakan yana yin amfani da wasu ya kunna wuta, ya kuma gasa nama a kai. Ya ci ya ƙoshi. yana ɗunɗuma kansa sai ya ce, "Ah, na ji ɗumi, na ga wutar."
\v 17 Sauran itatuwan da suka rage kuma sai ya yi allah da su, siffar da ya sassaƙa kuma; sai ya rusuna masa yana ba shi girma, sai ya yi addu'a gare shi yana cewa, "Cece ni, gama kai ne allahna."
\v 19 Babu mai yin tunani, ko su yi nazari su ce, "Daga cikin katakon na yi abin wuta da wasu; I, kuma na gasa gurasa bisa garwashin. Na gasa nama bisa garwashin na ci. To ya ya zan ɗauki sauran katakon da ya rage in yi abin ƙazanta da shi domin sujada? Ya ya zan rusuna ga wani kututturen katako?"
\v 20 Ya yi kamar toka ya ke ci; ruɗaɗɗiyar zuciyarsa ta sa ya kauce. Baya iya ceton kansa, ko kuwa ya ce, "Wannan abin da ke hannun damana ba allahn gaskiya ba ne."
\v 23 Ku raira, ku sammai, gama Yahweh ya yi wannan; ku yi sowa, ku zurfafan duniya. Ku fashe da waƙa, ku tsunuka, kai daji da duk itatuwan da ke cikinka; gama Yahweh ya fanshi Yakubu, kuma za ya nuna ɗaukakarsa a Isra'ila.
\v 24 Wannan ne abin da Yahweh yace, mai fansarka, wanda ya yi ka daga cikin mahaifa: "Ni ne Yahweh, wanda ya yi dukkan abubuwa, wanda shi kaɗai ya shimfiɗa sammai, shi kaɗai ya sarrafa duniya.
\v 25 Ni wanda na lalata kayan tsafin masu maganar wofi na kuma wulaƙanta masu karanta kayan tsafin; Ni wanda na juyarda hikimar masu hikima na kuma maida shawararsu wawanci.
\v 26 Ni, Yahweh, wanda ke tabbatarda maganganun bawansa wanda kuma ke sa hasashen manzanninsa su afku, wanda ya cewa Yerusalem, 'Za a sake zaunawa a cikinki,' da kuma garuruwan Yahuda, 'Za a sake ginaku, kuma zan ɗaga rusassun wurarensu';
\v 28 Yahweh ne ya faɗa game da Sairus, 'Makiyayina ne shi, za ya aiwatar da dukkan nufina; za ya zartar da doka game da Yerusalem, 'Za a sake ginata,' game da haikalin, 'Bari a sake kafa harsashensa.'"
\c 45
\cl Sura 45
\p
\v 1 Ga abin da Yahweh ya faɗi wa shafaffensa, ga Sairus, wanda nake riƙe da hannun damansa, domin inci ƙarfin al'ummai a gabansa, in tuɓe makaman sarakuna, in kuma buɗe ƙofofi a gabansa, domin ƙofofin su zauna a buɗe:
\v 8 Ku sammai, ku kwararo ruwa daga sama! bari sararin sammai su kwararo da adalci. Bari duniya ta shanyesu, domin ceto ya tsiro, da adalci kuma su yi girma tare. Ni, Yahweh, na halicce su dukka.
\v 9 Kaiton duk wani wanda ke gardama da wanda ya halicce shi, ga wanda ya ke kamar kowacce tukunyar yunɓu a cikin tukwanen yunɓu a ƙasa! yunɓun za ya iya cewa mai yin tukwanen, 'Me kake yi?' ko 'Aikin naka baya da abin riƙewa a jikinsa'?
\v 11 Ga abin da Yahweh yace, Mai Tsarki na Isra'ila, Mahaliccinka: 'Me yasa kake tambayoyi game da abin da zan yi domin 'ya'yana? zaka gaya mani abin da zan yi game da aikin hannuwana?'
\v 13 Na motsa Sairus cikin adalci, kuma zan miƙar da tafarkunsa dukka. Zai gina birnina; za ya bar mutanena 'yan gudun hijira su koma gida, ba kuma da farashi ba ko cin hanci,'" Yahweh mai runduna ya faɗa.
\v 14 Ga abin da Yahweh ya faɗa, "Za a kawo maku cinikayyar Masar da fataucin Itiyofiya tare da Sabiyawa, mutane masu doguwar siffa. Za su zama naku. Za su biyo ku, tafe cikin sarƙoƙi. Za su rusuna a gabanku suna roƙonku suna cewa, 'Tabbas Allah na tare daku, babu kuma wani sai dai shi.'"
\v 18 Ga abin da Yahweh ya faɗa, shi wanda ya halicci sammai, Allahn gaskiya wanda ya ƙirƙiro duniya, ya halittata, ya kafa ta. Ya halittata, ba a matsayin jujiba, Ya zãna ta domin a zauna a cikinta: "Ni ne Yahweh, babu wani kuma.
\v 19 Ban yi magana a asirce ba, a wani ɓoyayyen wuri; Ban cewa zuriyar Yakubu, 'Ku neme ni a wofi ba!' Ni ne Yahweh, Mai yin magana a gaskiya; Ina furta abubuwan da ke dai-dai.
\v 20 Ku tattaro kanku ku zo! ku taru wuri ɗaya, ku 'yan gudun hijira daga cikin al'ummai! basu da Ilimi, su waɗanda ke ɗaukar sassaƙaƙƙun siffofi su kuma yi addu'a ga allolin da ba su iya ceto.
\v 21 Ku zo kusa ku furta mani, ku kawo shaida! bari su yi mugun shirinsu tare. Wane ne ya nuna wannan tundã can? Wane ne ya yi shelar shi? Ba Ni ne ba, Yahweh? Babu wani Allah sai dai ni, Allah baratacce Mai ceto kuma; babu wani baya gare ni.
\v 23 Na yi rantsuwa da kaina, maganar dokar adalci tawa, kuma ba za ta koma baya ba: 'A gare ni kowacce gwiwa zata durƙusa kuma kowanne harshe za ya rantse.
\v 25 A cikin Yahweh dukkan zuriyar Isra'ila za su barata; za su yi taƙama a cikinsa.
\c 46
\cl Sura 46
\p
\v 1 Bel ta rusuna, Nebo ta sunkuya; an ɗauke gumakansu a bisa dabbobi da bisashen ɗaukar kaya. Waɗannan gumakai da kuka ɗauko kaya ne masu nauyi a bisa dabbobin da suka gaji.
\v 6 Mutane sukan zubo da zinari waje daga Jaka sukan kuma gwada azurfa a bisa ma'auni. Sai su yi hayar maƙeri, sai ya narka ya yi masu allah; sai su rusuna su kuma yi mashi sujada.
\v 7 Za su ɗagashi su ɗora a kafaɗa su ɗaukeshi; sai su ajiye a wurin zamansa, zai tsaya a wurin zamansa ba kuma zai matsa daga wurin ba. Za su yi kuka zuwa gare shi, amma ba za ya iya amsawa ba ko kuwa ya ceci wani daga matsalarsa.
\v 11 Na kira tsuntsun ganima daga gabas, mutumin dana zaɓa kuma daga ƙasa mai nisa; I, na faɗa; Zan kuma aiwatar da shi; ina da manufa, zan kuma aikata.
\v 6 Na yi fushi da mutanena; na lalata gãdona na miƙasu cikin hannunki, amma ba ki nuna masu jinƙai ba; ki ka ɗora kaya mai nauyi bisa tsofaffin mutanen.
\v 7 Ki ka ce, "Zan yi mulki har abada a matsayin sarauniya ni kaɗai." ba ki yi la'akari da abubuwannan ba a zuciyarki, ba ki kuwa duba yadda za su kasance ba.
\v 8 To yanzu saurari wannan, ke da kika ƙaunaci annashuwa kika zauna a tsare; ke da kika ce a zuciyarki, "Zan wanzu, babu kuma wani kamar ni; Bazan taɓa zaunawa kamar gwauruwa ba, ko in taɓa fuskantar rashin 'ya'ya ba."
\v 9 Amma abubuwan nan biyu za su zo maki a lokaci guda a rana ɗaya: rashin 'ya'ya da gwauranci; da cikakken ƙarfi za su afko maki, duk da sihirinki da surkullen ki masu yawa da layunki.
\v 10 Kin dogara ga muguntarki; ki ka ce, "Babu mai gani na"; hikimarki da iliminki sun kai ki ga hallaka, amma kika ce a zuciyarki, "Na wanzu, babu kuma wani kama da ni."
\v 11 Bala'i za ya afko maki; ba za ki iya korar shiba da surkullenki. Lalacewa zata faɗo maki; ba za ki iya kawar da ita ba. Babbar hasara zata afko maki nan da nan, kafin ki farga.
\v 12 Ki yi naciya wurin zuba magungunanki da sihirorinki mãsu yawa waɗanda kika yi aminci wurin nanatawa tun cikin kuruciyarki; watakila za ki yi nasara, watakila za ki kori bala'in.
\v 13 Kin gaji da yawan zuwa wurin bokayenki; bari su waɗannan mutanen su tashi su ceceki - su waɗanda ke shawagi a sammai suna duba taurari, waɗanda ke furta sabobbin watanni - bari su ceceki daga abin da zaya faru dake.
\v 14 Duba, za su zama kamar haki, wuta za ta cinye su. Ba za su ceci kan su ba daga cikin harsashen. Babu garwashin da za su ji ɗumi dashi babu kuma wutar da za su zauna a gefe!
\v 15 Ga abin da za su zama a gare ki, su waɗanda kika yi aiki tare da su, kika yi saye da sayarwa tare da su da ki na yarinya, dukkansu kuma su ka ci gaba da aikata abubuwansu na wawanci; da kika yi kukan neman taimako kuma, ba bu wanda zai iya ƙwato ki."
\c 48
\cl Sura 48
\p
\v 1 Ku saurara, ya gidan Yakubu, waɗanda a ke kira da suna Isra'ila, waɗanda kuma kuka fito daga tsatson Yahuda; ku da kuka yi rantsuwa da sunan Yahweh kuka kuma tono Allahn Isra'ila, amma bada gaske ba ko kuma ta hanyar adalci.
\v 5 domin wannan na furta waɗannan abubuwa tuntuni; kafin su faru na sanardaku, domin kada ku ce, 'Gunkina ya yi wannan,' ko kuwa 'Sassaƙaƙƙen siffana ko sarrafaffen siffar ƙarfena ya ƙaddara waɗannan abubuwa.'
\v 6 Kun ji game da waɗannan abubuwa; ku duba dukkan alamunnan; kuma ku, ba za ku yarda da cewa abin da na faɗi gaskiyane ba? Daga yanzu zuwa nan gaba, zan nunamaku sabobbin abubuwa, ɓoyayyun abubuwan da ba ku sani ba.
\v 8 Ba ku taɓa ji ba; ba ku sani ba; ba a bayyana abubuwan nan a kunnuwanku ba kafin yanzu. Domin na san ku macutane sosai, kuma ku masu taurinkai ne tunda a ka haife ku.
\v 14 Ku tattara kanku, dukkanku, ku saurara! wane ne a cikinku ya yi shelar waɗannan abubuwa? Wanda Yahweh ya zaɓa za ya cika nufinsa a kan Babila. Za ya aiwatar da nufin Yahweh a kan Kaldiyawa.
\v 16 Ku zo kusa da ni, ku saurari wannan: Tun daga farko ban yi magana a asirce ba; sa'ad da ya faru, ina nan." Yanzu Ubangiji Yahweh ya aike ni, da Ruhunsa kuma.
\v 17 Ga abin da Yahweh, Mai fansarku, Mai tsarki na Isra'ila ya faɗa, "Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ke koya maku yadda za ku yi nasara, wanda ke bida ku a hanyar da za ku bi.
\v 19 Da yawan zuriyarku yakai kamar rairayi, 'ya'ya kuwa daga mahaifarku kamar ƙwayoyin rairayi; da baza a datse sunansu ba ko kuwa a gogesu daga gabana.
\v 20 Ku fito daga Babila! ku tsere daga Kaldiyawa! da ƙarar kuka mai ƙaraurawa ku yi shelar shi! ku sanar da wannan, ku sa ya bazu zuwa iyakar duniya! Ku ce, 'Yahweh ya fanshi bawansa Yakubu.'
\v 1 Ku saurare ni, ku dake gaɓar tekuna! ku kasa kunne gare ni, ku manisantan mutane. Yahweh ya kira ni tun da a ka haife ni da suna na, sa'ad da mahaifiyata ta kawo ni cikin duniya.
\v 4 Amma sai na ce, "Koda ya ke nayi zaton nayi aiki a banza, na ɓata karfina a banza, duk da haka adalcina yana ga Yahweh, kuma sakamakona na gun Allahna."
\v 5 Yanzu Yahweh ya yi magana - wanda ya sifanta ni daga haihuwata in zama bawansa, za ya maida Yakubu kuma gare shi, domin a tattaro Isra'ila zuwa gare shi, gama an ɗaukaka ni a gaban Yahweh, kuma Allahna ya zama ƙarfina -
\v 6 sai ya ce, "Abu mafi ƙanƙanta kai ka zama bawana da zan sa ya sake kafa kabilun Yakubu, ya kuma farfaɗo da tsirarrun Isra'ila. Zansa ka zama haske ga Al'ummai, domin ka zama cetona ga duk karshen duniya."
\v 7 Wannan ne abin da Yahweh yace, mai 'Fansar Isra'ila, Mai Tsarkin Nan nasu, gare shi wanda a ka rena ransa, al'ummai suka ƙi shi, da kuma barorin masu mulki, "Sarakuna za su ganka su miƙe, kuma "hakimai za su ganka su rusuna, saboda Yahweh mai aminci ne, wato Mai Tsarkin nan na Isra'ila, wanda ya zaɓe ka."
\v 8 Ga abin da Yahweh ya faɗi, "A lokacin dana shirya nuna tagomashina zan ba ka amsa, kuma a ranar ceto zan taimake ka; zan yi maka kariya, in kuma bada kai a matsayin alƙawari domin mutanen, domin a sake gina ƙasar, a kuma sake raba gãdon da ya lalace.
\v 9 Za ka cewa 'yan kurkuku, 'Ku fito waje;' ga waɗanda ke ramuka masu duhu, 'Ku nuna kanku.' Za su yi kiwo a hanyoyi, kuma dukkan sararin gangare zai zama makiyayarsu.
\v 10 Ba za su ji yunwa ko ƙishi ba, ko kuwa zafi ko rana ta buge su, domin shi mai yi masu jinƙai zai jagorance su; zai bishe su har ga maɓulɓulan ruwa.
\v 13 Ku yi waƙa, sammai, da murna, duniya; fashe da waƙoƙi ku duwatsu! Gama Yahweh zai ta'azantar da mutanensa, ya kuma ji tausayin nãsa masu tsanancin wahala.
\v 15 Mace za ta iya mantawa da jaririnta, da ke shan nononta, har ta rasa jin tausayin ɗan da ta haifa? I, za su iya mantawa, amma Ni ba zan manta daku ba.
\v 18 Duba kewaye ki gani, suna tattarowa suna zuwa gare ki. Lallai hakika idan ina raye - wannan Yahweh ne ya faɗa -za ki sa su kamar kayan ado, ki kuma sanya su kamar amarya.
\v 19 Koda shi ke ke lalatacciya ce kuma kufai, ƙasa ce da dã a ka hallakar, yanzu za ki yiwa mazaunan ƙasar ƙanƙanta, kuma masu takura maki za su yi nisa dake.
\v 20 'Ya'yan da a ka haifa a lokacin da a ka yi maki rashi za su faɗa a kunnuwanki, 'Wurin ya yi mana ƙanƙanta, a yi mana ƙãri, saboda mu zauna a nan.'
\v 21 Sa'an nan za ki tambayi kanki, 'Wane ne ya haifi waɗannan 'ya'yan domina? An yi mani rashi kuma ni bakarariya ce, mai gudun hijira da sakakkiya ni ke. Wane ne ya yi renon waɗannan yaran? Duba, ni kaɗai a ka bari; daga ina waɗannan suke?"'
\v 22 Wannan ne abin da Ubangiji Yahweh yace, "Duba, Zan tayar da hannuna ga al'ummai; Zan tayar da tutar alamata ga mutane. Za su zo da 'ya'yanki maza a hannuwansu su kuma taho da 'ya'yanki mata a kafaɗunsu.
\v 23 Sarakuna za su zama kamar ubanninki, kuma sarauniyoyinsu kamar masu renonki; za su rusuna maki da fuskokinsu ƙasa suna lasar ƙurar ƙafafunki; kuma za ki san cewa ni ne Yahweh; waɗanda suke jira na ba za su kunyata ba."
\v 25 Amma ga abin da Yahweh yace, "I, za a karɓe kamammun daga jarumi, kuma a washe ganimar; Gama zan yi tsayayya da magabcinki in kuma ceci 'ya'yanki.
\v 26 Zan ciyar da masu tsananta maku da naman jikinsu; kuma za su bugu da jininsu, kamar a ce ruwan inabin ne. Sai dukkan 'yan adam su sani cewa Ni, Yaweh, ne mai cetonku da mai fansarku, Maɗaukaki na Yakubu."
\c 50
\cl Sura 50
\p
\v 1 Wannan ne abin da Yahweh ya faɗi, "Ina takardar saki da na saki mahaifiyarku? ga waɗanne masu bina bashi na sayar daku? Duba, an sayar daku domin laifofinku ne, domin kuma tayarwarku, a ka kori mahaifiyarku.
\v 2 Me yasa na zo amma babu kowa a wurin? Me yasa na yi kira amma babu wanda ya amsa? Hannu na ya gajarce ga fansar ku ne? Ko babu iko a gare ni da zan ƙuɓutar da ku? Duba, ga tsautawata na busar da teku; na maida koguna hamada; kifayensu suka mutu domin rashin ruwa suka ruɓe.
\v 4 Ubangiji Yahweh ya bani harshe kamar na ɗaya daga cikin waɗanda a ka koyar dasu, saboda in yi maganar ƙarfafawa ga gajiyayyu; yana farkar da ni daga safiya zuwa safiya; ya kan tasar da kunnena ga saurarawa kamar waɗanda a ka koyar dasu.
\v 7 Gama Ubangiji Yahweh zai taimake ni; saboda haka ba zan wulaƙanta ba; don haka na maida fuskata kamar dutsen ƙyastawa, domi na san ba zan kunyata ba.
\v 8 Shi wanda zai yi mani adalci yana kusa, Wane ne zai yi jayayya da ni? Bari mu tsaya mu fuskanci juna. Wane ne mai tuhuma ta? Bari ya zo kusa da ni.
\v 10 Wane ne a cikinku ke tsoron Yahweh? Wane ne ke biyayya da muryar bawansa? Wa ke tafiya a cikin zurfafan duhu ba tare da haske ba? Sai ya dogara da sunan Yahweh ya kuma jingina ga Allahnsa.
\v 11 Ku duba, dukkan ku masu kunna wuta, masu tanadawa kansu cociloli: ku yi tafiya cikin hasken wuta da harsunan wutar da kuka kunna. Wannan ne abin da ku ka karɓa daga gare ni: za ku kwanta a wurin azaba.
\c 51
\cl Sura 51
\p
\v 1 Ku saurare ni, ku da ke biɗar ayyukkan adalci, ku dake neman Yahweh: Ku dubi dutsen da aka sassaƙo ku da kuma mahaƙar duwatsu inda aka yanko ku.
\v 3 I, Yahweh zai ta'azantar da Sihiyona; zai ta'azantar da dukkan kufanta; jejinta ya maida kamar gonar Iden, kuma sararin hamadarta a gefen kogin Yodan ya maida kamar lambun Yahweh; za a sami farinciki da murna a cikinta, godiya, da ƙarar waƙa.
\v 6 Ku ɗaga idanuwanku ga sararin sama, sai ku kalli duniya a ƙasa, gama sammai za su ɓace kamar hayaƙi, duniya za ta shuɗe kamar tufa, kuma mazaunanta za su mutu kamar ƙudaje. Amma cetona zai ci gaba har abada, gama adalcina ba zai taɓa daina aiki ba.
\v 7 Ku saurare ni, ku da kuka san abin da ya ke dai-dai, ku dake da dokokina a zukatanku: kada ku ji tsoron zage-zagen mutane, ko ku karaya saboda wulaƙancinsu.
\v 8 Gama ƙwaro mai cin kaya zai cinye su kamar tufafi, tsutsa kuma ta cinye su kamar ulu; amma adalci na zai dawamma har abada, cetona kuma ga dukkan tsararraki."
\v 9 Farka, farka, ka suturtar da kanka da ƙarfi, damtsen Yahweh. Tashi kamar kwanakin dã, tsararraki na zamanan dã. Ba kai ba ne ka ragargaza Rahab, kai da ka soke dodon ruwa?
\v 11 Waɗanda Yahweh ya fansa za su dawo su zo Sihiyona tare da kukan farinciki tare kuma da murna har abada a kawunansu; kuma murna da farinciki za su mallake su, baƙinciki da makoki za su tsere daga gare su.
\v 13 Donme ku ka mance da Yahweh wanda ya yi ku, wanda ya miƙar da sammai ya kuma kafa harsasan duniya? Kun kasance a cikin fargaba kowacce rana saboda zafin fushin mai zalunci sa'ad da ya shirya ya yi hallaka. Ina hasalar mai zaluncin?
\v 16 Na sa maganata a bakinka, kuma na rufe ka da inuwar hannuna, domin in dasa sammai, in kafa harsasan duniya, in kuma cewa Sihiyona, 'ku mutanena ne.'"
\v 17 Farka, farka, tashi tsaye Yerusalem, ke da kika bugu a hannun Yahweh daga kwanon fushinsa; ke da kika bugu daga kwanon, har zuwa dago-dago daga ƙoƙon tangadi.
\v 18 Babu kowa a cikin dukkan 'ya'yanta maza da ta haifa da zai yi mata jagora; babu kowa kuma daga cikin 'ya'yanta maza waɗanda ta rayar da su da zai riƙe hannunta.
\v 22 Ubangijinki Yahweh, Allahnki wanda ke kãriyar ki ya ce, "Duba, na ɗauki ƙoƙon tangaɗi daga hannun ki -kwanon, wadda shi ne ƙoƙon fushi na. domin kada ki sake shan sa kuma.
\v 23 Zan sa shi a hannun masu ba ki wuya, waɗanda suka ce maki, 'Ki kwanta a ƙasa don mu yi tafiya bisan ki; kin maida bayanki kamar ƙasar da a ke takawa, kamar kuma tituna domin su yi tafiya akai."
\c 52
\cl Sura 52
\p
\v 1 Farka, farka, ki sa ƙarfinki, Sihiyona; ki sa sababbin tufafinki, Yerusalem, Birni mai tsarki, gama marasa kaciya da kazamtattu ba za su sake shigar ki ba.
\v 5 Yanzu me nake da shi a nan - wannan furcin Yahweh ne - ganin an ɗauke mutane na babu dalili? Waɗanda suke mulkinsu suka yi ba'a - Wannan furcin Yahweh ne - kuma aka ci gaba da saɓon suna na dukkan rana.
\v 7 Yaya kyaun sawayen manzo mai kawo labarai ma su daɗi ya ke akan duwatsu, wanda ke shelar salama. wanda ke riƙe da saƙonni masu daɗi, wanda ya shelar ceto, wanda ya cewa Sihiyona, "Allahnki na mulki!"
\v 12 Gama ba za ku tafi a cikin hanzari ba, ko ku tafi a cikin fargaba ba; gama Yahweh zai tafi gabanku; kuma Allah na Isra'ila zai kasance a bayanku.
\v 14 Kamar yadda da yawa suka yi fargaba da kai - kamanninsa ya lalace fiye da kowanne mutum, kuma fasalinsa bai sake yin kama da wani abu na mutum ba.
\v 15 Duk da haka, bawa na zai yayyafa al'ummai masu yawa sarakuna kuma za su rufe bakunansu saboda shi. Gama abin da ba a taɓa faɗa masu ba, za su gani, kuma abin da ba su taɓa ji ba, za su gane.
\c 53
\cl Sura 53
\p
\v 1 Wane ne ya gaskata da abin da ya ji daga gare mu, kuma ga wane ne aka bayyana hannun Yahweh?
\v 2 Gama ya yi girma a gaban Yahweh kamar 'yar itaciya, kuma kamar tsiro daga cikin busasshiyar ƙasa; ba shi da wani kyakkyawan jamali ko daraja; sa'ad da muka ganshi, babu wani kyau da zai rinjaye mu.
\v 3 Mutane suka rena shi suka kuma ƙi shi; mutumin baƙinciki, kuma wanda ya saba da raɗaɗi. Kamar wanda mutane ke ɓoye fuskarsu daga gare shi; aka rena shi; muka kuma ɗauke shi ba a bakin komai ba.
\v 4 Amma tabbas ya sungumi cututtukanmu ya kuma ɗauke baƙincikinmu; duk da haka mun yi zaton cewa Allah ne ke hukunta shi, Allah ya mazge shi, ya kuma azabta.
\v 5 Amma an soke shi saboda ayyukan tayarwarmu; aka ragargaje shi saboda zunubanmu. Hukunci domin salamarmu ya kasance a kansa, kuma ta wurin raunukansa muka warke.
\v 7 An muzguna masa; duk da haka sa'ad da ya ƙasƙantar da kansa, bai buɗe bakinsa ba; kamar ɗan ragon da za'a kai yanka, kuma kamar tumakin dake tsaye shiru a gaban masu sausaya, haka shi ma bai buɗe bakinsa ba.
\v 8 Ta wurin wulaƙantarwa da hukuntawa aka kayar da shi; wane ne daga wancan tsara ya sake yin tunani a kansa? Amma an datse shi daga ƙasar masu rai; saboda laifuffukan mutanena aka yanke masa hukunci.
\v 10 Duk da haka, nufin Yahweh ne a murkushe shi a sa shi ciwo. Sa'ad da ya mai da kansa baiko domin zunubi, zai ga 'ya'yansa, zai daɗa tsawon kwanakinsa, kuma dalilin Yahweh zai cika ta wurinsa.
\v 12 Saboda haka zan ba shi nasa kason a cikin yawan mutane, kuma zai raba ganimar da mutane da yawa, domin ya sa kansa ga mutuwa, aka kuma ƙidaya shi tare da masu kurakurai. Ya ɗauki zunuban mutane da yawa ya kuma yi roƙo domin masu kurakurai.
\c 54
\cl Sura 54
\p
\v 1 "Yi waƙa, ke bakarariya, ke da ba ki haihu ba; ki fashe da waƙar farinciki ki yi kuka da karfi, ke da ba ki taɓa yin naƙudar haihuwa ba. Gama 'ya'yan yasassa sun fi na matar da aka aura," inji Yahweh.
\v 4 Kada ki ji tsoro domin ba za ki ji kunya ba, ko ki karaya ba gama ba za a wulaƙanta ki ba; za ki mance da abin kunyar kuruciyarki da wulaƙancin yashewarki.
\v 5 Gama wanda ya Yiki shi ne mijinki; Yahweh mai runduna shi ne sunansa. Mai Tsarkin nan na Isra'ila shi ne mai Fansarki; Shi a ke kira Allahn dukkan duniya.
\v 6 Gama Yahweh ya sake kirawo ki a matsayin matar da aka yasar da take kuma cikin ƙunci a ruhu. Kamar matar da a kuruciyarta aka aurota sa'an nan aka ƙi ta," inji Allahnki.
\v 8 A sa'ad da na yi fushi mai zafi, na ɓoye fuskata daga gare ki na wani lokaci; amma da madawwamin alƙawari aminci zan yi maki jinƙai - inji Yahweh, wanda ya ƙubutar dake.
\v 9 Gama wannan kamar ruwayen Nuhu ne a gare ni: kamar yadda na rantse cewa ruwayen Nuhu ba za su sake shan kan duniya ba, saboda haka na rantse cewa ba zan yi fushi dake ko in kwaɓe ki ba.
\v 10 Koda shi ke tsaunuka za su iya faɗuwa kuma tuddai su girgizu, duk da haka madawwamiyar ƙauna ta ba zata rabu da ke ba, ko alƙawarin salamata ya girgiza ba - inji Yahweh, wanda ke yi maki jinƙai.
\v 14 A cikin adalci zan sake kafa ku. Ba za ku ƙara fuskantar tsanantawa ba, gama ba za ku ji tsoro ba; kuma ba abin ban tsoro da zai yi kusa da ku ba.
\v 17 Babu makamin da aka ƙera gãba da kai da zai yi nasara; kuma zan kayar da duk wanda ya tuhume ka. Wannan shi ne gădon bayin Yahweh, kuma kariyarsu daga gare ni take. wannan furcin Yahweh ne."
\c 55
\cl Sura 55
\p
\v 1 Ku zo, kowannen ku dake jin kishin ruwa, ku zo wurin ruwan, ku da baku da kuɗi, ku zo, ku saya, ku ci, ku zo ku sayi ruwan inabi da madara kyauta da arha kuma.
\v 2 Me ya sa kuke auna azurfa domin abin da ba abinci ba, kuma me yasa kuke aiki domin abin da ba ya ƙosarwa? Ku saurare ni sosai ku ci abin dake da kyau, ku kuma yi farinciki cikin ƙoshi.
\v 3 Ku juyo da kunnuwanku ku zo gare ni! Ku saurara, domin ku rayu! Zan yi madawwamin alƙawari da ku - ingantacce, amintacciyar ƙauna dana alƙawarta wa Dauda,
\v 5 Duba, za ku kira ga al'umman da baku san su ba; kuma al'umman da basu san ku ba za su rugo gunku saboda Yahweh Allahnku, Mai Tsarki na Isra'ila wanda ya ɗaukaka ku."
\v 7 Bari mai mugunta ya bar tafarkinsa, haka nan mai zunubi ya bar tunane-tunanensa. Bari ya komo wurin Yahweh, sai ya yi masa jinƙai, da kuma Allahnmu wanda zai gafarta masa a yalwace.
\v 10 Gama kamar yadda ruwa da ƙanƙara ke saukowa daga sama, kuma basu komawa sai sun jiƙa ƙasa, susa amfaninta su tsiro su bada 'ya'ya ga manomin da ya yi shuka ya kuma bada abinci ga mai ci,
\v 11 haka nan ne maganata wadda ta fito daga bakina zata kasance - ba za ta komo gare ni a banza ba, amma zata yi nasara a kan abin da na aike ta ta aiwatar.
\v 12 Gama za ku fita da farinciki, a kuma jagorance ku a cikin salama; Tsaunuka da tuddai za su farfashe da murnar ihu a gabanku, kuma dukkan itatuwan filaye za su tafa hannuwansu.
\v 13 A maimakon ƙayoyin saura, itatuwa masu ganyaye za su fito; kuma a maimakon itacen ƙaya, itacen ganye mai kyau zai fito, kuma zai zama domin Yahweh, domin sunansa, kamar madawwamiyar alama da ba za a tsige ba."
\c 56
\cl Sura 56
\p
\v 1 Wannan shi ne abin da Yahweh ya faɗi, "Ku yi abin dake dai-dai; ku yi abin da ya kamata; gama cetona ya yi kusa, kuma adalcina na gaf da bayyana.
\v 2 Mai albarka ne mutumin dake yin wannan, wanda kuma ya riƙe shi kam-kam. Ya kiyaye ranar Asabaci, ba ya ƙazamtata, yana kuma kiyaye hannunsa daga aikin mugunta."
\v 5 dominsu ne zan kafa alama a cikin gidana da ganuwata abin tunawa da yafi samun 'ya'ya maza da mata. Zan ba su madawwamin abin tunawa da ba za a taɓa datsewa ba.
\v 6 Haka ma bãƙin da suka haɗa kansu da Yahweh - su ɓauta masa, waɗanda kuma suke son sunan Yahweh, su ɓauta masa, duk wanda ke lura da Asabaci, da wanda ke kãre kansa daga ƙazamta, da wanda ya riƙe alƙawari na kam-kam
\v 7 - zan kawo su ga tsarkakken tsaunina in sa su yi farinciki a gidan addu'a ta; baye-bayensu na ƙonawa da hadayunsu za su samu karɓuwa a bagadina. Gama za'a kira gidana gidan addu'a domin dukkan al'ummai,
\v 10 Dukkan matsaransu maƙafi ne, ba su fahimta ba. Su dukka karnuka dake shiru ne waɗanda ba su iya yin haushi. Suna mafarki, kuma a kwance suna ƙaunar yin barci.
\v 11 Karnukan na da babban marmarin ci; Ba za su taba samun abin da ya ishe su ba; su makiyaya ne da ba su da ganewa; dukkansu sun juya ga ta su hanya, kowannensu na ƙyashin mugun ribar kansa.
\v 12 "Zo," suka ce "bari mu sha ruwan inabi da barasa mai karfi," Gobe zai zama kamar yau, rana mai girma fiye da yadda a ke tsammani."
\c 57
\cl Sura 57
\p
\v 1 Adali ya hallaka, babu wanda ya kula, kuma mutanen amintaccen alƙawari sun taru a can, amma ba wanda ya gane cewa an ɗauke mai adalici ne daga mugunta.
\v 5 Kuna ɗuma kanku ku da kuke kwance tare ƙarƙashin itacen rimi, ƙarƙashin kowanne koren itace, ku dake kashe 'ya'yanku a cikin rafuffukan da suka ƙone da ƙarƙashin duwatsu masu maratayi
\v 6 A cikin abubuwa masu laushi na rafin gangare su ne aka ba ku. Wato kayan ibadarku. Kun zuba ruwan baikon abin sha gare su kuka kuma ɗaga baikon hatsi. A waɗannan abubuwan ne ya kamata in ji daɗi?
\v 8 A bayan ƙofa da ƙyaurayen kuka shirya alamunku; kun yashe ni, kun yi wa kanku tsiraici, sai kuka haura sama; kuka yi gadonku da faɗi. Kuka yi yerjejeniya da su; kuka ƙaunaci gadajensu; kuka ga tsiraicinsu.
\v 11 Wane ne kuke damuwa dominsa? Wane ne kuke jin tsoronsa da yawa har ya sa kuka aikata abin ruɗi, harma kun manta da ni ko ku yi tunani akai na? Saboda na yi shiru na dogon lokaci, harma yanzu kun dena jin tsoro na.
\v 13 Sa'ad'da kuka yi kũka, bari tarin gumakanku su 'yantar daku. Maimakon haka iska za ta ɗauke su dukka, wani numfashi zai ɗauke su dukka. Duk da haka wanda ya yi mafaka a cikina zai gaje ƙasar ya kuma mallaki tsarkakken tsaunina.
\v 15 Gama ga abin da mai girma maɗaukaki Kaɗai yace, wanda ke zaune har abada, wanda sunansa tsarki ne, "Ina zaune a maɗaukakin wuri mai tsarki, tare da shi kuma mai karyayye da ƙasƙantaccen ruhu, in falkar da ruhun masu ƙasƙantar da kai, in farkar da zuciyar masu tawali'u.
\v 17 Saboda da zunubinsa na ribar ƙwãce, Na yi fushi, Na kuma hukunta shi; Na ɓoye fuskata na kuma yi fushi, amma ya koma da baya cikin hanyar zuciyarsa.
\v 2 Duk da haka suna nema na kullum suna kuma fahariya a sanin hanyoyina, kamar al'umma dake yin aɗalci da ba su yashe da dokokin Allahnsu ba. Suna tambayata hukuncin aɗalci; Suna jin daɗin tunani a kan Allah ya kusance su.
\v 3 Me yasa muka yi azumi,' suka ce, 'amma ba ka gani ba? Me yasa muka ƙasƙantar da kanmu, amma ba ka kula ba?' Duba, a ranar azuminku, kuna neman jin daɗinku kuna kuma danne dukkan ma'aikatanku,
\v 5 Wannan shi ne lallai irin azumin da zan so: Ranar da wani zai ƙasƙantar da kansa, ya sunkuyar da kansa kamar ciyawa, kuma ya yafa tsummokara da toka a ƙarƙashinsa? Kun tabbata za ku kira wannan azumi, rana wadda ta gamshi Yahweh?
\v 6 Wannan ba shi ne azumin dana zaɓa ba: A saki miyagun sarƙoƙi, a kwance igiyoyin karkiya, a sa waɗanda aka ragargaza su sami 'yanci, a kuma karya kowacce karkiya?
\v 7 Ko kuma ku raba gurasarku da mayunwata ku kuma shigo da marasa mazauni cikin gidanku ba?" Idan ku ka ga wani tsirara, sai ku suturtar da shi; kuma kada ku ɓoye kanku daga 'yan'uwa.
\v 9 Sa'an nan ne za ku yi kira, kuma Yahweh zai amsa; za ku yi kukan neman taimako, kuma zai ce, "Ga ni nan." Idan har kuka ɗauke daga tsakiyarku karkiya, da zargi, da maganganun mugunta,
\v 10 idan ku da kanku kuka tanada wa mayunwata kuma kuka biya buƙatun gajiyayyu; sa'an nan ne haskenku zai keto daga cikin duhu, kuma duhunku zai zama kamar rana tsaka.
\v 11 Sa'an nan Yahweh zai jagoranceku a kullum kuma ya ƙosar da ku a wuraren da babu ruwa, ya kuma ƙarfafa ƙasusuwanku. Za ku zama kamar lambu mai laima, kuma kamar maɓulɓular ruwa, wanda ruwansa ba ya ƙarewa.
\v 12 Waɗansunku za su sake gina lalatattun kufaye; za ku tada kufayen tsararraki da yawa; za a kira ku "Masu gyaran Garu," "Masu maido da titunan da za a zauna."
\v 13 Dãma a ce kun juyo da ƙafafunku daga tafiya a ran Asabaci, kuma daga yin abin son ranku a ranata mai tsarki. Dãma a ce kun kira ranar Asabaci abin farinciki, kuma harma ku kira sha'anin Yahweh tsarki da martaba. Dãma a ce kun girmama ranar Asabacina wurin barin sha'anin kanku, ku kuma bar neman jin daɗin kanku da kuma kun ƙi faɗar maganganun kanku.
\v 14 Sa'an nan za ku yi farinciki cikin Yahweh; kuma zan sa ku yi yawo a ƙwalƙwolin duniya; zan ciyar daku daga gãdon Yakubu mahaifinku - gama bakin Yahweh ya faɗa."
\c 59
\cl Sura 59
\p
\v 1 Duba, hannun Yahweh bai gajarce bada ba zai iya ceto ba; kunnensa bai kurmance ba, da ba zai iya ji ba.
\v 6 sãƙarsu ba za a iya yin tufafi da su ba, kuma ba za su iya rufe kansu da ayyukansu ba. Ayyukansu ayyukan zunubi ne, kuma ayyukan ta'addanci na cikin hannayensu.
\v 8 Ba su san tafarkin salama ba, kuma babu adalci a tafarkinsu. Sun ƙago karkatattun tafarkuna; Duk wanda ya yi tafiya kan waɗannan tafarku ba zai san salama ba.
\v 9 Saboda haka adalci ya yi nesa daga gare mu, kuma ayyukan adalci ba su kai wurinmu ba. Mun jira haske, amma muna ganin duhu; muna neman haske amma muna tafiya a duhu.
\v 10 muna laluɓar bango kamar maƙafi, kamar waɗanda basu gani. Mu na yin tuntuɓe da rana kamar da asussuba; a cikin jarumai muna kama da matattun mutane.
\v 13 Mun yi tayarwa, muna musanta Yahweh kuma mun juya daga bin Allahnmu. Mun faɗi yaudara da juyin baya, mun ɗauki cikin gunaguni daga zuciya da maganganun ƙarya.
\v 19 Saboda haka za su ji tsoron sunan Yahweh daga yamma, da ɗaukakarsa daga fitowar rana; gama zai zo kamar rafi mai kwararowa, wand numfashin Yahweh ke tunkuɗawa.
\v 21 Ni dai, wannan shi ne alƙawari na da su - inji Yahweh - ruhuna wanda ya ke bisanku, da maganganuna waɗanda na sa a bakinku, ba za su bar bakinku ba, ko su fita daga bakin 'ya'yanku, ko su fita daga bakin 'ya'yan 'ya'yanku ba - inji Yahweh - daga wannan lokaci zuwa har abada."
\c 60
\cl Sura 60
\p
\v 1 Tashi, haskaka; gama haskenki ya iso, kuma ɗaukakar Yahweh ta taso a bisanki.
\v 5 Sa'an nan za ki duba ki cika da farinciki, kuma zuciyarki zata yi ambaliya, domin za a zuba maki yalwar teku, kuma arzikin al'ummai za su zo gare ki.
\v 6 Ayarin raƙuma za su rufe ki, takarkaran Midiyan da Ifa; dukkansu za su zo daga Sheba; za su kawo zinari da kayan ƙanshi, kuma za su raira waƙar yabon Yahweh.
\v 7 Dukkan garkunan Kedar za a tara maki, ragunan Nebayot za su biya buƙatunki; za su zama karɓaɓun baiko a kan bagadina; kuma zan darjanta gidana mai daraja.
\v 9 Ƙasashen gãɓar tekuna suna nema na, kuma jiragen ruwa na Tarshish suna jagoranci, domin su kawo 'ya'yanki maza daga nesa, zinariyarsu da azurfarsu na tare da su, domin sunan Yahweh Allahnki, da kuma domin Mai Tsarkin Nan na Isra'ila, saboda ya daukaka ki.
\v 10 'Ya'ya maza na bãƙi za su gina garunki, kuma sarakunanki za su yi maki bauta; koda ya ke a cikin fushina na hore ki, duk da haka a cikin alheri na zan yi maki jinƙai.
\v 14 Za su zo gare ki su yi rusuna, 'ya'yan ki maza waɗanda suka ƙasƙantar dake; za su rusuna a ƙafafunki; za su kira ki Birnin Yahweh, Sihiyona ta Mai Tsarkin Nan na Isra'ila.
\v 15 A maimakon ki ci gaba da zaman wadda aka yashe ta aka ƙita, ba kuma wanda ya wuce ta wurinki, zan maishe ki abin fahariya na har abada, abin murna daga tsara zuwa tsara.
\v 16 Za ki kuma sha madarar al'ummai, kuma za a rene ki a kirjin sarakuna; za ki sani cewa Ni, Yahweh, ni ne Mai cetonki da mai Fansarki. Mai Girman nan na Yakubu.
\v 17 A maimakon tagulla zan kawo maki zinariya, a maimakon ƙarfe zan kawo azurfa; a maimakon katako, tagulla, kuma a maimakon duwatsu, karfe. Zan sa salama ta zama gwamnoninki, adalci kuma masu mulkinki.
\v 19 Rana ba za ta ƙara zama haskenki da rana ba, ko hasken wata ya haskaka a kanki; amma Yahweh zai zama haskenki na har abada, Allahnki kuma shi ne darajarki.
\v 1 Ruhun Ubangiji Yahweh na bisana, domin Yahweh ya shãfe ni in yi shelar labari mai daɗi ga ƙuntattu. Ya aike ni in warkar da waɗanda suka karye a zuci, in yi shelar 'yanci ga kamammu, da kuma buɗewar kurkuku domin waɗanda suke a ɗaure.
\v 3 Ya aike ni - in ba masu makoki cikin Sihiyona - in ba su rawani a maimakon toka, mai na farinciki a maimakon makoki, alƙyabba ta yabo a maimakon ruhun baƙinciki, domin a kira su rimayen adalci, dashen Yahweh, domin ya sami ɗaukaka.
\v 4 Za su sạke gina rusassun birane nadã; za su gyara lalatattun wurare. Za su gyara rusassun birane, lalatattu tun daga tsararrakin da suka rigaya suka wuce.
\v 7 A maimakon kunyar ki zaki sami riɓi biyu; kuma a maimakon ƙasƙanci za su yi farinciki da rabonsu. Haka za su sami riɓi biyu na rabon ƙasarsu; murna zata zama tasu har abada.
\v 9 Zuriyarsu za su zama sanannu a cikin dukkan al'ummai, kuma 'ya'yan tsatsonsu cikin mutane. Dukkan wanda ya gan su zai tabbatar da su, cewa su ne mutanen da Yahweh ya sawa albarka.
\v 10 Zan yi farinciki sosai cikin Yahweh; cikin Allahna zan yi murna sosai. Gama ya suturce ni da mayafan ceto; ya suturceni da rigar adalci, kamar yadda ango ke ƙawata kansa da rawani, kuma kamar yadda amarya takan ƙawata kanta da kayan ado.
\v 11 Gama kamar yadda ƙasa take fito da dashe-dashenta, kuma kamar yadda gona takan sa shuke-shukenta su tsiro, haka Ubangiji Yahweh zai sa adalci da yabo su tsiro a gaban dukkan al'ummai.
\c 62
\cl Sura 62
\p
\v 1 Saboda Sihiyona ba zan yi shuru ba, saboda da kuma Yerusalem ba zan yi tsit ba, har sai adalcinta ya bayyana da haske sosai, kuma cetonta kamar fitila mai ci bal-bal.
\v 4 Ba za a ƙara ce dake, "Yasasshiya" ba; ko ƙasarki ba za a ce da ita, "Watsattsiya ba." Hakika, za a ce dake "Farincikina na cikin ta," ƙasarki kuma "Aurarra," gama Yahweh na farinciki dake, kuma ƙasarki za ta yi aure.
\v 5 Hakika, kamar yadda saurayi matashi yakan auri 'yar budurwa, haka 'ya'yanki za su aure ki, kuma kamar yadda ango ke farinciki da amaryarsa, Allahnki zai yi farinciki dake.
\v 8 Yahweh ya yi rantsuwa da hannunsa na dama da kuma hannunsa mai iko, "Hakika ba zan ƙara bada hatsinki ya zama abinci ga maƙiyanki ba. Bãƙi ba za su sha sabon ruwan inabinki ba, wanda ke kika aikinta ba.
\v 9 Gama waɗanda suka yi girbin hatsinsu za su ci su kuma yabi Yahweh, kuma waɗanda suka tsinke 'ya'yan inabisu za su sha ruwan inabin a cikin wurarena masu tsarki."
\v 10 Ku shigo, ku shigo ta cikin ƙofofi! Ku shirya hanya domin mutane! Ku gina, ku gina babbar hanya! Ku tattara duwatsu! Ku tada tutar alama sama domin al'ummai!
\v 11 Duba, Yahweh yana sanarwa zuwa ga iyakar duniya, "Ku cewa ɗiyar Sihiyona: Duba, Mai cetonki yana zuwa! Ki gani, ladarsa na tare da shi, kuma sakamakonsa ya sha gabansa."
\v 12 Za su kira ki, "tsarkakakkiyar jama'a; fansassu na Yahweh," kuma za a kira ki "Biɗaɗɗiya; birnin da ba a yashe shi ba."
\c 63
\cl Sura 63
\p
\v 1 Wane ne wannan da ya ke zuwa daga Idom, yafe da jar tuffa daga Bozara? Wane ne shi cikin kayan sarauta, yana takawa da ƙarfin hali sabili da girman ƙarfinsa? Ni ne, ina maganar adalci da kuma ikon yin ceto.
\v 3 Na tattaka 'ya'yan inabi a matatsar inabi ni kaɗai, kuma babu wani daga cikin al'ummai da ya yi tare da ni. Na tattakesu a cikin fushina na kuma rugurgujesu cikin hasalata. Jininsu ya ɗiɗɗiga a kan kayana kuma ya ɓaɓɓata tufafina.
\v 5 Na duba, kuma babu wani da zai yi taimako. Na yi mamaki cewa babu mai taimako, amma hannuna ya kawo mani nasara, kuma fushina mai tsanani ya iza ni.
\v 7 Zan faɗi amincin ayyukan alƙawarin Yahweh, ayyukan yabo na Yahweh. Zan faɗi dukkan abin da Yahweh ya yi mana, da kuma manyan alherinsa zuwa gidan Isra'ila. Wannan tausayi da ya nuna mana sabili da jinƙansa, da kuma ayyuka masu yawa na amintaccen alƙawarinsa.
\v 9 Cikin dukkan wahalarsu, shima ya wahala, sai mala'ika daga gare shi ya cecesu. Cikin ƙaunarsa da jinƙansa ya cecesu, ya kuma ɗagasu sama ya kuma bishesu a cikin dukkan zamanan dã.
\v 11 Mutanensa suka yi tunani game da kwanakin dã na Musa. Suka ce, "Ina Allah, wanda ya fito da su daga teku da makiyayin garkensa? Ina Allah, wanda ya sanya Ruhunsa Mai Tsarki a cikinsu?
\v 15 Ka duba daga sama ka kuma kula daga wurinka mai tsarki da kuma maɗaukakin mazauni. Ina himmarka da kuma manyan ayyukanka? Tausayinka da ayyukan juyayinka an hana mana su.
\v 16 Gama kai ne ubanmu, ko da shi ke Ibrahim bai sanmu ba, kuma Isra'ila bai fahimcemu ba, kai, Yahweh, kai ne ubanmu. 'Mai fansarmu' sunanka kenan tun zamanan dã.
\v 17 Yahweh, me yasa ka sạmu muka bijire daga hanyoyinka ka kuma taurare zukatanmu, har ba mu yi maka biyayya ba? Ka dawo ta dalilin bayinka, kabilun gãdonka.
\v 2 kamar yadda wuta ke chinye ƙananan kurmi, ko wuta tasa ruwa ya tafasa. Ai ya, dãma dai sunanka ya zama sananne a wurin magabtanka, domin al'ummai su yi rawar jiki a gabanka!
\v 5 Ka kan zo ka taimaki waɗanda suke farinciki da aikata abin dake na adalci, su dake tunawa da hanyoyinka suna kuma yin biyayya dasu. Kạ yi fushi a lokacin da muka yi zunubi. Ta hanyoyinka kullum za a cecemu.
\v 6 Gama dukkan mu mun zama kamar wanda ya ƙazamtu, kuma dukkan aikin adalcinmu kamar tsumman jinin haila. Dukkanmu mun yi yaushi kamar ganyaye; kurakuranmu, kamar iska, sun kwashe mu nesa.
\v 7 Babu ko ɗaya mai kira bisa sunanka, wanda ya ke ƙoƙarin ya kama ka. Gama ka ɓoye fuskarka daga gare mu ka kuma sa muka lalace a cikin hannun kurakuranmu.
\v 12 Ta ƙaƙa za ka jure wannan, Yahweh? Ta ƙaƙa za kayi shuru ka kuma ci gaba da ƙasƙantar damu?
\c 65
\cl Sura 65
\p
\v 1 "Na shirya da su same ni su waɗanda ba su tambaya ba; Na shirya domin su same ni su waɗanda ba su neme ni ba. Na ce, 'Ga ni nan! Ga ni nan!' ga al'ummar da ba su kira bisa sunana ba.
\v 2 Na miƙa hannayena dukkan yini zuwa ga mutane masu taurin zuciya, masu tafiya a cikin tafarkin da ba dai-dai ba, waɗanda suka yi tafiya bisa ga tunaninsu da shirye-shiryensu!
\v 7 domin zunubansu da zunuban ubanninsu tare," Yahweh ya faɗa. "Zan sãka masu domin ƙona turare a bisa tsaunuka da kuma ba'ar da suke yi mani a bisa tuddai. Saboda haka zan auna masu ayyukansu na dã a cikin cinyarsu."
\v 8 Ga abin da Yahweh ke cewa, "Kamar yadda a ke samun ruwan inabi daga nonon 'ya'yan inabi, lokacin da wani na cewa, 'Kada ka lalata shi, gama akwai abu mai kyau a cikinsa; Ga abin da zan yi domin barorina: Ba zan lallatar da su dukka ba.
\v 9 Zan fito da zuriya daga Yakubu, kuma daga Yahuda waɗanda za su mallaki tsaunukana. Zaɓaɓɓuna za su mallaki ƙasar, kuma bayina za su zauna a wurin.
\v 11 Amma ku da kuka yashe da Yahweh, waɗanda suke mantawa da tsaunina mai tsarki, masu shirya teburi domin allahn Sa'a, su kuma cika moɗar ruwan inabi mai gauraye domin Ƙaddara.
\v 12 Zan ƙaddara ku ga takobi, kuma dukkanku za ku rusuna ga kisa, domin a lokacin da nayi kira, ba ku amsa ba; da nayi magana, ba ku saurara ba. Amma ku ka aikata abin dake mugu a gabana kuka kuma zaɓi ku aikata abin da ba zan ji daɗinsa ba."
\v 13 Wannan shi ne abin da Ubangiji Yahweh ke faɗi, "Duba, bayina za su ci, amma ku za ku ji yunwa; duba, bayina za su sha, amma ku za ku ji ƙishi; duba, bayina za su yi murna, amma ku za ku kunyata.
\v 14 Duba, bayina za su yi sowa da farinciki domin murnar zuciya, amma ku za ku yi kuka saboda da zafin zuciya, kuma za ku yi makoki saboda karayar ruhu.
\v 16 Duk wanda ya furta albarka ga ƙasar zaiyi albarka ta wurina, Allah na gaskiya. Duk wanda ya yi rantsuwa a duniya zai rantse da ni, Allah na gaskiya, gama matsalolin dã za a manta da su, gama za su ɓoye daga idanuna.
\v 18 Amma ku za kuyi murna da farinciki har abada a cikin abin da zan hallita. Ga shi, ina dab da halitta Yerusalem abin farinciki, mutanenta kuma abin fahariya.
\v 20 Ba zai ƙara faruwa ba ɗan jinjiri ya rayu kwanaki kaɗan; ko tsohon mutum ya mutu kafin lokacinsa. Wanda ya mutu yana shekara ɗari za a ce da shi matashi. Duk wanda ya kãsa kaiwa shekara ɗari za a ɗauke shi la'ananne ne.
\v 22 Ba za su ƙara gina gida wani daban ya zauna ciki ba; ba za su shuka, wani ya ci ba; gama kamar kwanakin itatuwa haka zai zama kwanakin jama'ata. Zaɓaɓɓuna za su kere ayyukan hannuwansu a shekaru.
\v 25 Damisa da ɗan rago za su yi kiwo tare, kuma zaki zai ci ciyawa kamar sã; amma ƙura ce za ta zama abincin maciji. Ba za su ƙara cutarwa ko su hallakar a kan dukkan tsaunina mai tsarki," inji Yahweh.
\c 66
\cl Sura 66
\p
\v 1 Wannan shi ne abin da Yahweh ya ke cewa, "Sama kursiyina ne, ƙasa kuma matashin sawuna. To ina gidan da za ku gina mani? Ina wurin da zan iya hutawa?
\v 2 Hannuwana suka yi dukkan waɗannan abubuwa; haka waɗannan abubuwa suka zo suka kasance - wannan shi ne abin da Yahweh ya furta. Wannan shi ne mutumin dana zaɓa, karyayye da tawali'u a ruhu, kuma wanda ya ke rawar jiki ga maganata.
\v 3 Shi wanda ya yanka rago ya kuma kashe mutum; shi wanda ya yi hadayar ɗan rago ya kuma karya wuyan kare; shi wanda ya miƙa baikon hatsi ya miƙa jinin alade; shi wanda ya miƙa turare na tunawa shima yasa wa mugunta albarka. Sun zaɓi hanyoyin kansu, kuma suna fahariya da aikin ƙazamtarsu.
\v 4 Ni ma haka zan zaɓi masu horonsu; zan kawo a bisansu abin nan da suke tsoro, domin a lokacin dana yi kira, ba bu wanda ya amsa; dana yi magana, ba bu wanda ya saurara. Suka aikata abin da ke mugu a gabana, suka zaɓi su yi abin dake ɓata mani rai."
\v 5 Ku saurara ga maganar Yahweh, ku da kuke rawar jiki da maganarsa, "Yan'uwanku da suka ƙi ku suka ware ku sabili da sunana suka ce, 'Bari Yahweh ya ɗaukaka, sa'an nan za mu ga murnar ku'; amma za a kunyatar dasu.
\v 8 Wane ne ya taɓa jin abu kamar haka? Wane ne ya taɓa ganin abubuwa kamar haka? Ana iya haihuwar al'umma a rana ɗaya? Al'umma tana iya haihuwa a ɗan ƙanƙanin lokaci? Duk da haka da Sihiyona ta shiga naƙuda, nan da nan ta haifi 'ya'yanta.
\v 9 Zan kawo jinjiri a cikin ƙofar fita in kuma hana a haifi jaririn?- Yahweh yana tambaya. Ko ina kawo jariri lokacin haihuwa amma sai in hana shi fitowa?- Allahnka na tambaya."
\v 12 Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Ina gab da zubo wadata bisanta kamar kogi, kuma arzikin al'ummai kamar ambaliyar kogi. Za kuyi reno kusa da ita, a ɗauke ku cikin hannuwanta, a karkaɗa ku da murna a gwuiwarta.
\v 14 Za ku ga wannan, kuma zuciyarku za tayi farinciki, kuma ƙasusuwanku za su tsiro kamar 'yan ciyayi. Za a bayyana hannun Yahweh ga bayinsa, amma zai nuna fushinsa gãba da maƙiyansa.
\v 17 Sun keɓe kansu suna tsabtace kansu, domin su shiga gonaki, suna bi ta tsakiyar waɗanda suke cin naman alade da abubuwan ban ƙyama kamar kũsu. "Za su kawo ga ƙarshe - wannan shi ne furcin Yahweh.
\v 18 Gama na san ayyukansu da tunaninsu. Lokaci na zuwa da zan tara dukkan al'ummai da yarurruka. Za su zo su ga ɗaukakata.
\v 19 Zan sa gaggarumar alama a tsakaninsu. Sa'an nan zan aiko da masu tsira daga gare su zuwa ga al'ummai: Zuwa ga Tarshish, Fut, da Lud, masu harbi da suke jan bakansu, zuwa ga Tubal, da Yaban, da kuma zuwa iyakar ƙasashen bakin ruwa da ke nesa inda ba su taɓa ji game da ni ko suka ga ɗaukakata ba. Za su furta ɗaukakata a tsakiyar al'ummai.
\v 20 Za su dawo da dukkan 'yan'uwanku daga cikin al'ummai, abin baiko ga Yahweh. Za su zo bisa dawakai, da karusai, da cikin kekunan shanu, da bisa jakuna, da kuma bisa raƙuma, zuwa ga tuduna mai tsarki Yerusalem - inji Yahweh. Gama jama'ar Isra'ila za su kawo baiko na hatsi a cikin kwanuka masu tsabta cikin gidan Yahweh.
\v 21 Zan zaɓi wasu daga cikinsu su a matsayin firistoci da kuma Lebiyawa - inji Yahweh
\v 22 Gama kamar yadda sabuwar sammai da sabuwar duniya da zan halitta za su dawwama a gabana - wannan shi ne furcin Yahweh - haka zuriyarku za su dawwama.
\v 23 Daga wata ɗaya zuwa na gaba, kuma daga wannan Asabaci zuwa na gaba, dukkan mutane za su zo su rusuna mani - inji Yahweh.
\v 24 Za su fito waje su dubi gawawakin jama'ar da su ka yi mani tayarwa, gama tsutsotsin da za su ci su ba za su mutu ba, kuma wutar da za ta haɗiyesu ba za ta ɓice ba; kuma za su zama abin ƙi ga dukkan masu rai."