ha_tw/bible/kt/hades.md

1.6 KiB

Lahira

Ma'ana

Kalmar nan "Lahira" an more su a cikin Littafi Mai Tsarki domin ayi batun mutuwa da kuma wurin da rayukan mutane zasu bayan sun mutu. Ma'anarsu ɗaya ce.

  • Kalmar "Lahira" a Ibraniyanci an fi amfani da ita a cikin Tsohon Alƙawari domin a baiyana inda matattu suke.
  • A cikin Sabon Alƙawari, kalmar Girkanci "Hades" tana magana ne akan wurin da rayukan mutanen da suka tayar wa Allah za su kasance. A kan ce waɗanan rayukan za'a tura su can "ƙarƙas" zuwa Hades. A waɗansu lokuta wanan ya saɓawa tafiya zuwa "sama" inda rayukan mutanen da suka yi biyayya ga Allah za su kasance.
  • Kalmar nan "Hades" tattare take dakalmar "mutuwa" a cikin littafin Wahayin Yahaya. A lokuta na ƙarshe, da Hades da mutuwa duk za'a zuba su cikin tafki nija wuta, wadda ita ce jahannama.

Shawarwarin Fassara:

  • Kalmar nan "Lahira" a cikin Tsohon Alƙawari za'a iya fassara ta da "wuri na mutuwa" ko "wuri na rayukan matattu." Waɗansu Fasssarori na fassara shi da "rami" ko "mutuwa" ya danganta dai ga wurin.
  • Kalmar "Hades" a Sabon Alƙawari za'a iya fassara ta da wurin da rayukan marasa bada gaskiya za su zauna" ko wuri na azaba ga matattu" ko wuri na mutanen da basu bada gaskiya ba."
  • Waɗansu fassarori suna moron kalmomin "Lahira" da "Hades" suna rubuta su a matsayin rami bisa ga furcin harshensu.
  • Za'a iya ƙarawaɗansu 'yan harufa ga kowanen su domin yin bayani a kan su, misali na yin haka su ne "Lahira, wurin da matattu suke" da "Hades kuma wuri ne na mutuwa."

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Ayyukan Manzanni 02:31
  • Farawa 44:29
  • Yona 02:2
  • Luka 10:15
  • Luka 16:23
  • Matiyu 11:23
  • Matiyu 16:18
  • Wahayin Yahaya 01:18