ha_tw/bible/other/nation.md

2.0 KiB

al'umma, al'ummai

Ma'ana

Al'umma babbar ƙungiyar mutane ce da suke da wasu sharuɗɗan mulki. Yawancin lokaci mutanen da suka zama al'umma sun fito ne daga zuriya ɗaya da kuma yare ɗaya.

  • Yawancin lokaci "al'umma" na da tsarin al'adunta da kuma iyakar ƙasarta.
  • A cikin Littafi Mai Tsarki "al'umma" zata iya zama ƙasa (kamar Masar ko Itiyofiya), amma dai yawancin lokaci ana nufin ƙungiyar mutane ne, tunbane in ana ambatonsu da yawa. Da mahimmanci a duba nassi.
  • Al'ummai a cikin Littafi Mai Tsarki sun haɗa da waɗannan: Isra'ilawa, Filistiyawa, Asiriyawa, Babiloniyawa, Kan'aniyawa, Romawa, Girik, da dai sauransu.
  • Wani lokaci kalmar nan "al'umma" ana amfani da ita a kwatanta zuriyar wasu ƙungiyar mutane, kamar lokacin da Allah ya gaya wa Rebeka cewa 'ya'ya maza da zata haifa "al'umma biyu" ce da za su yi faɗa da junansu. Za a iya fassara wannan haka "za su kafa al'umma biyu" ko "kakannin ƙungiyar mutane biyu."
  • Wannan kalma da aka fassarata zuwa "al'ummai" wani lokaci ana amfani da ita a kira "waɗanda ba yahudawa ba" ko "mutanen da ba sa bauta wa Yahweh". Yawancin lokaci yadda aka yi ammfani da ita a nassi yakan fid da ma'anar a sarari.

Shawarwarin Fassara:

  • Ya danganta ga nassi, wannan kalma "al'umma" za a iya fassara ta haka "ƙungiyar mutane" ko "mutane" ko "ƙasa."
  • Idan yaren na da wata kalma domin "al'umma" da ya sha bamban da waɗannan to, sai suyi amfani da ita duk lokacin da ta sake maimaita kanta a cikin Littafi Mai Tsarki indai ya shiga nassi dai-dai kuma ba matsala.

Wannan kalma da ta nuna yawa "al'ummai" za a iya fassara ta a ce "ƙungiyar mutane."

(Hakanan duba: Asiriya, Babila, Kan'ana, Al'ummai, Girik, ƙungiyar mutane, Filistiyawa, Roma)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Taski:

  • 1 Tarihi 14:15-17
  • 2 Tarihi 15:06
  • 2 Sarakuna 17:11-12
  • Ayyukan Manzanni 02:05
  • Ayyukan Manzanni 13:19
  • Ayyukan Manzanni 17:26
  • Ayyukan Manzanni 26:04
  • Daniyel 03:04
  • Farawa 10:2-5
  • Farawa 27:29
  • Farawa 35:11
  • Farawa 49:10
  • Luke 07:05
  • Markus 13:7-8
  • Matiyu 21:43
  • Romawa 04:16-17