ha_tw/bible/other/12tribesofisrael.md

1.0 KiB

kabilu sha biyu na Isra'ila, kabilu sha biyu na 'ya'yan Isra'ila, kabilu sha biyu

Ma'ana

Wannan kalma, "kabilu sha biyu" na nufin 'ya'ya maza sha biyu na Yakubu da zuriyarsu.

  • Yakubu jikan Ibrahim ne. Daga baya Allah ya sauya masa suna daga Yakubu zuwa Isra'ila.
  • Waɗannan sune sunayen kabilun: Ruben, Simiyon, Lebi, Yahuda, Dan, Naftali, Gad, Asha, Issaka, Zebulun, Yosef da Benyamin.
  • Zuriyar Lebi basu gaji wata ƙasa ba a Kan'ana domin su kabilar firitoci ne waɗanda aka keɓe domin bauta wa Allah da mutanensa.
  • Yosef ya sami rabo biyu na ƙasar gãdo, waɗanda aka miƙa wa 'ya'yansa biyu maza, Ifraim da Manasse.
  • Akwai wurare da dama a Littafi Mai Tsarki inda jerin sunayen kabilun sha biyu sun banbanta kaɗan. Wani lokaci Lebi, Yosef, ko Dan ba a sa shi cikin jerin kuma wani lokacin 'ya'yan Yosef biyu maza Ifraim da Manasse ana sa su a jerin.

(Hakanan duba: gãji, Isra'ila, Yakubu, firist, kabila)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Ayyukan Manzanni 26:07
  • Farawa 49:28
  • Luka 22:28-30
  • Matiyu 19:28