ha_tw/bible/names/zephaniah.md

589 B

Zefaniya

Gaskiya

Zefaniya, ɗan Kushi, annabi ne wanda ya zauna a Yerusalem ya kuma yi anabci ̀̀̀a zamanin mulkin Sarki Yosiya. Ya yi rayuwa a zamani ɗaya da Irmiya.

  • Ya tsauta wa mutanen Yahuda domin sun yiwa allolin ƙarya sujada. Annabce-anabcensa an rubuta su cikin littafin Zefaniya a Tsohon Alƙawari.
  • Akwai mutane dayawa waɗanda aka kira su da sunan Zefaniya a Tsohon Alƙawari, yawancinsu firistoci ne.

(Hakanan duba: Irmiya, Yosiya, firist)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • 2 Sarakuna 25:18
  • Irmiya 52:24-25
  • Zakariya 06:9-11
  • Zefaniya 01:03