ha_tw/bible/names/ur.md

602 B

Ur

Gaskiya

Ur birni ne mai muhimmanci a kusa da Kogin Yufiretis a tsohon yankin Kaldiya, wadda ke harɗe da Mesofotamiya. Wannan yankin na a ƙasar da aka sani yau da suna Iraƙ.

  • Ibrahim ya fito ne daga birnin Ur kuma daga nan ne Allah ya kirawo shi ya fito ya tafi zuwa ƙasar Kana'an.
  • Haran, ɗan'uwan Ibrahim da kuma mahaifin Lot, ya mutu a Ur. Wannan na iya zama dalilin da ya sa Lot ya bar Ur ya tafi tare da Ibrahim.

(Hakanan duba: Ibrahim, Kan'ana, Kaldiya, Kogin Yufiretis, Haran, Lot, Mesofotamiya)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Farawa 11:27-28
  • Farawa 11:31