ha_tw/bible/names/tirzah.md

824 B

Tirza

Gaskiya

Tiza wani birnin Kan'ana ne mai muhimmanci da Isra'ilawa suka cafke. Suna ne kuma na ɗiyar Giliyad, zuriyar Manasse.

  • Birnin yana lardin da kabilar Manasse suka mamaye. Ana kautata zaton cewa birnin yana kamar mil goma daga arewacin birnin Shekem.
  • Shekaru daga bisani, na ɗan wani lokaci Tirza ya zama babban birnin tarayyar masarautar arewa ta Isra'ila, a zamanin mulkin sarakuna huɗu na Isra'ila.
  • Tirza kuma ya zamanto suna ne na ɗaya daga cikin jikokin Manasse mata. Suka roƙi a basu kasonsu na ƙasar tunda mahaifinsu ya mutu kuma bashi da 'ya'ya maza da zasu yi gãdonsa kamar yadda yake a al'ada.

(Hakanan duba: Kan'ana, gãdo, masarautar Isra'ila, Manasse, Shekem)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Littafin Lissafi 27:1
  • Littafin Lissafi 36:11
  • Waƙar Suleman 06:4