ha_tw/bible/names/solomon.md

915 B

Suleman

Gaskiya

Suleman ɗaya daga cikin 'ya'yan sarki Dauda ne. Mahaifiyarsa ita ce Batsheba.

  • Lokacin da Suleman ya zama sarki, Allah ya ce masa ya roƙi duk abin da yake so. Sai Suleman ya roƙi hikima da zai iya mulkin jama'a da kyau da adalci. Allah ya yi farinciki da roƙon Suleman ya bashi hikima da wadata mai yawa.
  • Suleman ya zama sananne domin gina haikali a Yerusalem.
  • Koda yake Suleman ya yi mulki da hikima a shekarar farko ta mulkinsa, da ga baya ya yi rashin azancin auren matan bãƙi ya fara bautawa allolinsu.
  • Saboda rashin adalcin Suleman, bayan mutuwarsa Allah ya raba mulkin Isra'ila kashi biyu, Isra'ila da Yahuda. Waɗannan mulkokin sunyi ta yaƙar junansu.

(Hakanan duba: Batsheba, Dauda, Isra'ila, Yahuda, masarautar Isra'ila, haikali)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Ayyukan Manzanni 07:47-50
  • Luka 12:27
  • Matiyu 01:7-8
  • Matiyu 06: 29
  • Matiyu 12:42