ha_tw/bible/names/samson.md

937 B

Samsin

Gaskiya

Samsin na ɗaya daga cikin alƙalai, na Isra'ila. Ya fito daga kabilar Dan.

  • Allah ya baiwa Samsin karfi wanda ya fi na mutum, wanda ya yi amfani dashi domin ya yaƙi makiyan Isra'ila, Filistiyawa.
  • An sanya Samsin a ƙarƙashin alƙawari da ba zai aske gashin kansa ba ko kuma ya shã giya ko wani abin shã kumburarre. A duk sa'ad da yake kiyaye wannan alƙawari, Allah ya ci gaba da ikonta shi.
  • Daga nan ya saɓa wa alƙawarin da ya ɗauka ya bari aka aske gashin kansa, har Filistiyawa suka cafke shi.
  • Yayin da Samsin ke cikin bauta, Allah ya sake maido masa da ƙarfinsa ya kuma bashi damar ya hallakar da haikalin ƙazamin allah Dagon, tare da Filistiyawa masu yawan gaske.

(Hakanan duba: mai kuɓutarwa, Filistiyawa, kabilu goma sha biyu na Isra'ila)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Ibraniyawa 11:32-34
  • Littafin Alƙalai 13:25
  • Littafin Alƙalai 16:02
  • Littafin Alƙalai 16:31