ha_tw/bible/names/pontus.md

711 B

Fontus

Gaskiya

Fontus wani lardin Roma ne a lokacin mulkin Roma da Ikilisiya ta farko. An kafa ta ne a kudancin gaɓar Baƙin Teku, a arewacin yankin da yanzu ita ce ƙasar Turkaniya ko Toki.

  • Kamar yadda yake a rubuce a littafin Ayyukan Manzanni, mutane da suke daga lardin Fontus suna Yerusalem sa'ad da Ruhu Mai Tsarki ya fara zuwa ga manzanni a Ranar Fentikos.
  • Wani mai bada gaskiya mai suna Akila ya zo ne daga Fontus.
  • Lokacin da Bitrus yake rubuta wa Kiristoci dake warwatse cikin wurare daban-daban na yankin nan, Fontus na ɗaya daga cikin yankunan daya ambata.

(Hakanan duba: Akila, Fentikos)

Wuraren da za ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • 1 Bitrus 01:1-2
  • Ayyukan Manzanni 02:09