ha_tw/bible/names/phonecia.md

1.0 KiB

Fonishiya, Sarofonishiyawa

Gaskiya

A zamanin dã, Fonishiya al'umma ce mai wadata tana kafe a Kan'ana a gaɓar Tekun Baharmaliya arewa da Isra'ila.

  • Fonishiya ta kasance a yankin ƙasar dake yamma na wanda a yau ita ce ƙasar Lebanon.
  • A lokacin Sabon Alƙawari, cibiyar Fonishiya Taya ce. Wania kuma muhimmin birnin Fonishiya shi ne Sidon. Fonishiya na kusa da Siriya, saboda haka mutane daga wannan yankin ana ce da su "Sarofonishiyawa.
  • Fonishiyawa sanannun masassaƙa ne gwanaye suna amfani da itacen sida dake da yawa a ƙasarsu, domin kuma suna yin launin shunayya mai tsada, suna kuma da baiwar tafiya fatauci akan ruwa. Gwanaye kuma a gina kwale-kwalen ruwa.
  • Wani rubutu na tun farko mutanen Fonishiyawa ne suka ƙagoshi. An yi amfani da shi. Harufofin rubutunsu ya bazu ko'ina saboda cuɗanyarsu da ƙungiyoyin mutane da yawa ta wurin kasuwancinsu.

(Hakanan duba: sida, shunayya, Sidon, Tyre)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Ayyukan Manzanni 11:19-21
  • Ayyukan Manzanni 15:3-4
  • Ayyukan Manzanni 21:02
  • Ishaya 23:10-12