ha_tw/bible/names/philistines.md

783 B

Filistiyawa

Gaskiya

Filistiyawa wasu ƙungiyar mutane ne da suka zauna a yankin Filistiya a gaɓar Tekun Baharmaliya. Ma'anar sunansu "mutanen teku."

  • Akwai manyan biranen Filistiya guda biyar: Ashdod, Ashkelon, Ekron, Gat, da Gaza.
  • Birnin Ashdod yana arewacin sashen Filistiya, birnin Gaza kuma yana kudunta.
  • Alƙali Samson shahararren mayaƙi ne gãba da Filistiyawa, ya yi amfani da mafificin ƙarfi daga Allah.
  • Sarki Dauda yawancin lokaci yakan kai yaƙi ga Filistiyawa, har da lokacin da yake saurayi ya buge mayaƙin Filistiya, Goliyat.

(Hakanan duba: Ashdod, Ashkelon, Dauda, Ekron, Gat, Gaza, Goliyat, Tekun Gishiri)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • 1Tarihi 18:9-11
  • 1 Sama'ila 13: 04
  • 2 Tarihi 09:25-26
  • Farawa 10:11-14
  • Zabura 056:1-2