ha_tw/bible/names/peter.md

827 B

Bitrus, Simon Bitrus, Kefas

Gaskiya

Bitrus yana ɗaya daga cikin manzannin Yesu guda goma sha biyu. Shi shugaba ne mai mahimmanci a ikilisiya ta farko,

  • Kafin Yesu ya kira shi ya zama almajirinsa, sunan Bitrus Siman ne.
  • Daga baya Yesu ya kira shi "Kefas," ma'ana "dutse" a harshen Aramaik. Ma'anar sunan Bitrus "dutse" a harshen Grik.
  • Allah ya yi aiki ta wurin Bitrus ya warkar da mutane ya kuma yi wa'azin labari mai daɗi akan Yesu.
  • Litattafai biyu a cikin Sabon Alƙawari wasiƙu ne da Bitrus ya rubuta domin ya ƙarfafa ya kuma koyar da 'yan'uwa masu bada gaskiya.

(Hakanan duba: almajiri, manzanni)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Ayyukan Manzanni 08;25
  • Galatiyawa 02:6-8
  • Galatiyawa 02:12
  • Luka 22:58
  • Markus 03:16
  • Matiyu 04:18-20
  • Matiyu 08:14
  • Matiyu 14:30
  • Matiyu 26:33-35