ha_tw/bible/names/persia.md

897 B
Raw Permalink Blame History

Fasiya, Fasiyawa

Gaskiya

Fasiya ƙasa ce wadda ita ma ta zama babbar mulki mai iko wadda Sairus Mai Girma ya kafa a shekara ta 550 BC. Ƙasar Fasiya tana kudu maso gabas da Babiloniya da kuma Asiriya a yankin da yau ake ce da shi Iran.

  • Mutanen Fasiya ana ce da su "Fasiyawa."
  • A ƙarƙashin dokar Sarki Sairus, aka 'yantar da Yahudawa daga bautar talala a Babila aka yardar masu su tafi gida, kuma aka sake gina haikali a Yerusalem, da kuɗin da mulkin Fasiya ya tanada.
  • Sarki Atazazas shi ne mai mulkin sarautar Fasiya lokacin da Ezra da Nehemiya suka koma Yerusalem domin su sake gina ganuwoyin Yerusalem.
  • Esta ta zama sarauniyar mulkin Fasiya lokacin data auri Sarki Ahasurus.

(Hakanan duba: Ahasurus, Atazazas, Asiriya, Babila, Sairus, Esta, Ezra, Nehemiya)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • 2 Tarihi 36:20
  • Daniyel 10:13
  • Esta 01:3-4
  • Ezekiyel 27:10