1.3 KiB
1.3 KiB
Obadiya
Gaskiya
Obadiya wani annabi ne a Tsohon Alƙawari da ya yi annabci gãba da Idom, zuriyar Isuwa. Akwai kuma maza da yawa da ake kiran su Obadiya cikin Tsohon Alƙawari.
- Littafin Obadiya shi ne mafi gajarta a cikin Tsohon Alƙawari ya kuma faɗi wani wahayi da Obadiya ya karɓo a mafarki daga Allah.
- Ba a sani ba sosai sa'ad da Obadiya ya yi rayuwa ya kuma yi anabci. Mai yiwuwa a lokacin mulkin waɗannan ne: Yoram, Ahaziya, Yowash, da Ataliya sarakunan Yahuda. Annabi Daniyel, Ezekiyel da Irmiya watakila sun yi annabci a wannan lokacin su ma.
- Watakila kuma Obadiya ya rayu har ya zuwa ƙarshen sarautar Sarki Zedekiya da kwashewa zuwa bautar talala a Babila.
- Wasu mutane masu suna Obadiya sune, wani zuriyar Saul, ba Gadiye da ya zama ɗaya daga cikin mazajen Dauda, da wani wanda ya zama shugaban masu hidima a fadar Sarki Ahab, da wani hakimin sarki Yehoshafat, da wani wanda ya taimaka wurin gyara haikali a zamanin Sarki Yosiya, da kuma wani Balebi mai tsaron ƙofa a zamanin Nehemiya.
- Mai yiwuwa marubucin littafin Nehemiya ɗaya ne daga cikin waɗannan mazaje.
(Hakanan duba: Ahab, Babila, Dauda, Idom, Isuwa, Ezekiyel, Daniyel, Gad, Yehoshafat, Yosiya, Lebi, Saul (Tsohon Alƙawari), Zedekiya)
Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:
- 1 Tarihi 03:21
- 1 Tarihi 08:38-40
- Ezra 08:8-11
- Obadiya 01:02