ha_tw/bible/names/nehemiah.md

904 B

Nehemiya

Gaskiya

Nehemiya Ba'isra'ile ne da dole ya tafi ƙasar Babiloniya sa'ad da Babiloniyawa suka kwashe mutanen Isra'ila da Yahuda zuwa bautar talala.

  • Lokacin da yake Mai shayarwa ga Sarkin Fasiya, Atazazas, Nehemiya ya roƙi sarki iznin ya koma Yerusalem.
  • Nehemiya ya bida Isra'ilawa a gina ganuwar Yerushalem wanda Babiloniyawa suka rushe.
  • Nehemiya yayi shekara goma sha biyu yana shugabanci a Yerusalem kafin ya koma fadar sarki.
  • Littafin Nehemiya a Tsohon Alƙawari ya bada labarin ayyukan Nehemiya na sake gina ganuwa da shugabantar da mutanen Yerusalem.
  • Akwai kuma wasu mutane masu sunan Nehemiya a Tsohon Alƙawari. Yawancin lokaci akan ƙara da sunan mahaifi domin a banbanta wane Nehemiyan ake magana a kai.

(Hakanan duba: Atazazas, Babila, Yerusalem, ɗa)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Ezra 02:1-2
  • Nehemiya 01:02
  • Nehemiya 10:03
  • Nehemiya 12:46