ha_tw/bible/names/mishael.md

961 B

Mishayel

Gaskiya

Mishayel sunan mutum uku ne a Tsohon Alƙawari.

  • Wani mutum da ake ce da shi Mishayel ɗan ɗan'uwan Harunan ne. Lokacin da Allah ya kashe 'ya'yan Haruna maza biyu bayan sun miƙa turare ta hanyar da Allah bai tsara masu ba, Mishayel da ɗan'uwansa aka basu hidimar ɗaukar gawawakin zuwa bayan sansanin Isra'ilawa.
  • Wani mutum kuma da ake ce da shi Mishayel ya tsaya a gefen Ezra lokaci da Ezra yake karanta littafin shari'a da aka binciko a gaban jama'a.
  • Lokacin da mutanen Isra'ila suke bautar talala a Babila, wani yaro matashi da ake kira Mishayel an kama shi shima kuma aka tilasta masa ya zauna a Babila. Babiloniyawa suka bashi suna, "Meshak." Da shi da abokansa, Azriya (shadrak) da Hananiya (Abednego), suka ƙi suyi sujada ga siffar sarki sai aka jefa su cikin tanderun wuta.

(Hakanan duba: Haruna, Azariya, Babila, Daniyel, Hananiya)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Daniyel 01:6-7
  • Daniyel 02:17-18