ha_tw/bible/names/midian.md

978 B

Midiyan, Bamidiye, Midiyawa

Gaskiya

Midiyan ɗan Ibrahim ne ta wurin matarsa Ketura. Kuma wannan sunan wasu ƙungiyar mutane ne da wani yanki dake Hamadar Arebiya ta Arewa wajen kudu da ƙasar Kan'ana. Mutanen ƙungiyar nan ana kiransu "Midiyawa."

  • Lokacin da Musa ya bar Masar da fari, ya tafi zuwa yankin Midiyan inda ya gamu da 'ya'ya mata na Yetro ya taimake su shayar da tumakinsu. Daga bisani Musa ya auri ɗaya daga cikin 'ya'ya mata na Yetro.
  • An kai Yosef Masar ta wurin wata ƙungiyar Midiyawa masu cinikin bayi.
  • Bayan shekaru masu yawa Midiyawa suka kai wa Isra'ilawa hari suka washe su cikin ƙasar Kan'ana. Gidiyon ya bida Isra'ilawa suka ci sua yaƙi.
  • Yawanci kabilun Arebiya na wannan zamani zuriyar waɗannan ƙungiyar ne.

(Hakanan duba: Arabiya, Masar, tumaki, Gidiyon, Yetro, Musa)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Ayyukan Manzanni 07:30
  • Fitowa 02:16
  • Farawa 25:1-4
  • Farawa 36:34-36
  • Farawa 37:28
  • Littafin Alƙalai 07:1