ha_tw/bible/names/manasseh.md

1.1 KiB

Manasse

Gaskiya

Akwai mutane biyar da ake kiransu da sunan Manasse a cikin Tsohon Alƙawari:

  • Manasse sunan ɗan farin Yosef ne.
  • Manasse da ƙanensa Ifraim Yakubu mahaifin Yosef ya karbe su tankar 'ya'yansa wannan ya ba zuriyarsu 'yancin zama cikin kabilu goma sha biyu na Isra'ila.
  • Zuriyar Manasse ta zama ɗaya daga cikin kabilun Isra'ila.
  • Yawancin lokaci ana kiran kabilar Manasse "rabin kabilar Manasse" domin wani sashen kabilar ne suka zauna a cikin ƙasar Kan'ana yamma da Kogin Yodan. Sauran kabilar suka zauna a gabashin Yodan.
  • Guda daga cikin sarakunan Yahuda shi ma ana kiransa Manasse.
  • Sarki Manasse mugun sarki ne wanda ya bada 'ya'yansa hadayar ƙonawa ga gumaku.
  • Allah ya hukunta Sarki Manasse ya bari abokan gãba suka cafke shi. Daga baya Manasse ya juyo ya rushe bagadai inda ake sujada ga gumaku.

(Hakanan duba: bagadi, Dan, Ifraim, Ezra, gumaka, Yakubu, Yahuda, al'ummai, kabilu goma sha biyu na Isra'ila)

Wuraren da ake samunsa a Littafi mai Tsarki:

  • 2 Tarihi 15:09
  • Maimaitawar Shari'a 03:12-13
  • Farawa 41:51
  • Farawa 48:1-2
  • Littafin Alƙalai 01:27-28