ha_tw/bible/names/lebanon.md

778 B

Lebanon

Gaskiya

Lebanon wata yankin ƙasa ce mai kyaun duwatsu a gaɓar Tekun Baharmaliya, arewa da Isra'ila. A lokacin Littafi Mai Tsarki wannan yanki kurmi ne cunkus da rimayen itatuwa kamar su sida da sifures.

  • Sarki Suleman ya aika ma'aikata Lebanon su saro itatuwan sida domin amfani da su a ginin haikalin Allah.
  • Lebanon ta dã da mazaunanta mutanen Fonisiya ne, ƙwararru a gine-ginen jiragen ruwa da ake amfani da su wajen kasuwanci masu armashi.
  • Birane Taya da Sidon suna cikin Lebanon. A waɗannan birane a cikin su ne aka fara amfani da rinin shunayya.

(Hakanan duba: sida, sifires, fir, Fonisiya)

Wuraren da ake samunsu a Littafi Mai Tsarki:

  • 1 Sarakuna 04:32-34
  • 2 Tarihi 02:8-10
  • Maimaitawar Shari'a 01:7-8
  • Zabura 029:3-5
  • Zakariya 10:8-10