ha_tw/bible/names/kadesh.md

992 B

Kadesh, Kadesh-Barniya, Meriba Kadesh

Gaskiya

Sunayen Kadesh, Kadesh-Barniya, Meriba Kadesh dukkansu na magana game da wani birni mai muhimmanci a tarihin Isra'ila wanda ke a sashen kudancin Isra'ila, kusa da lardin Idom.

  • Birnin Kadesh wani kurmi ne, wurin da akwai ruwa da ƙasa mai albarka a tsakiyar hamada mai suna Zin.
  • Musa ya aiki 'yan leƙen asirin ƙasa sha biyu zuwa ƙasar Kan'ana daga Kadesh Barniya.
  • Isra'ila kuma sunyi sansani a Kadesh a lokacin yawonsu cikin jeji.
  • A Kadesh Barniya ne Miriyam ta mutu.
  • A Meriba Kadesh ne Musa ya yi rashin biyayya da Allah ya kuma bugi dutsen domin ya samar wa Isra'ilawa ruwa, a maimakon yiwa dutsen magana kamar yadda Allah ya gaya masa.
  • Sunan "Kadesh" ya fito ne daga wata kalmar Ibraniyawa mai ma'ana "tsarki" ko "keɓaɓɓe."

(Hakanan duba: hamada, Idom, tsarki)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Ezekiyel 48:28
  • Farawa 14:7-9
  • Farawa 16:14
  • Farawa 20:1-3
  • Yoshuwa 10:40-41
  • Littafin Lissafi 20:1