1.1 KiB
1.1 KiB
Ayuba
Gaskiya
Ayuba mutum ne da aka yi bayaninsa a Littafi Mai tsarki a matsayin marar aibi mai adalci ne kuma a gaban Allah. Anfi saninsa domin jurewarsa a cikin bangaskiyarsa ga Allah a cikin lokuttan wahala mai tsanani.
- Ayuba yayi zama a ƙasar Uz, wadda ke wani waje gabas da ƙasar Kan'ana, watakila kusa da lardin Idomiyawa.
- Anyi tunanin cewa yayi rayuwa a zamanin Isuwa da Yakubu saboda ɗaya daga cikin abokan Ayuba shi "Batimaniye ne," wanda wata ƙungiyar mutane ce da aka yiwa suna bisa ga sunan jikan Isuwa.
- Littafin Ayuba a Tsohon Alƙawari ya zance game da yadda Ayuba da wasu suka dubi wahalarsa. Ya kuma bada yadda Allah a matsayin mahaliccin kowa da mai mulkin ko'ina ya kalli al'amarin.
- Bayan dukkan bala'o'in, daga bisani Allah ya warkar da Ayuba ya kuma sake ba shi 'ya'ya da dukiya.
- Littafin Ayuba na cewa ya tsufa sosai sa'ad da ya mutu.
(Hakanan duba: Ibrahim, Isuwa, ruwan ambaliya wato tsufana, Yakubu, Nuhu, ƙungiyar mutane)
Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:
- Ezekiyel 14:12-14
- Yakubu 05:9-11
- Ayuba 01:01
- Ayuba 03:05