ha_tw/bible/names/jerusalem.md

1.3 KiB

Yerusalem

Gaskiya

Yerusalem asalinsa tsohon birni ne na Kan'ana wanda daga bisani ya zama birni mafi muhimmanci a Isra'ila. Yana wajen kilomita 34 daga yamma da Tekun Gishiri kuma dai-dai arewa da Betlehem. Har wa yau shine babban birnin Isra'ila a yau.

  • Wannan suna "Yerusale"" an fara ambatonsa ne a cikin littafin Yoshuwa. Wasu sunayen wannan birni a Tsohon Alƙawari sun haɗa da "Salem", "birnin Yebus," da "Sihiyona." Dukka "Yerusalem" da "Salem," suna da tushen ma'anarsu na "salama."
  • Yerusalem asali tsararren wuri ne na Yebusiyawa da ake kira "Sihiyona" wanda Sarki Dauda ya ƙwato ya maida babban birninsa.
  • A Yerusalem ne Suleman ɗan Dauda ya gina haikali na farko a Yerusalem, bisa Tsaunin Moriya, wanda shine dutsen inda Ibrahim ya miƙa ɗansa Ishaku hadaya ga Allah. Aka sake gina haikalin a nan bayanda Babiloniyawa suka rushe shi.
  • Saboda haikalin na cikin Yerusalem, mayan bukukuwa na Yahudawa a nan ake shagalinsu.
  • Mutane sukan ce zamu "hau" zuwa Yerusalem tunda cikin duwatsu yake.

(Hakanan duba: Babila, Almasihu, Dauda, Yebusiyawa, Yesu, Suleman, haikali, Sihiyona)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Galatiyawa 04:26-27
  • Yahaya 02:13
  • Luka 04:9-11
  • Luka 13:05
  • Markus 03:7-8
  • Markus 03:20-22
  • Matiyu 03:06
  • Matiyu 04:23-25
  • Matiyu 20:17