ha_tw/bible/names/jeremiah.md

869 B

Irmiya

Gaskiya

Irmiya annabin Allah ne a masarautar Yahuda. Littafin Irmiya a Tsohon Alƙawari yana ɗauke da anabce-anabcensa.

  • Kamar yawancin annabawa, sau da yawa Irmiya na gargaɗin mutanen Isra'ila cewa Allah zai hukuntasu saboda zunubansu.
  • Irmiya yayi anabci cewa Babiloniyawa za su ƙwace Urshalima, yasa wasu mutanen Yahuda suka ji haushi. Sai suka sanya shi cikin wata rijiya mai zurfi, busasshiya suka barshi nan ya mutu. Amma sarkin Yahuda ya umarci bayinsa su je su ceto shi daga rijiyar.
  • Irmiya ya rubuta cewa yayi fatan a ce ma idanunsa su zama "maɓulɓular hawaye," domin ya bayyana zurfin ɓacin ransa bisa kangara da wahalhalun mutanensa.

(Hakanan duba: Babila, Yahuda, annabi, kangara, rijiya)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • 2 Tarihi 35:25
  • Irmiya 01:02
  • Irmiya 11:01
  • Matiyu 02:18
  • Matiyu 16:13-16
  • Matiyu 27:10