ha_tw/bible/names/hittite.md

957 B

Bahitte, Hittiyawa

Gaskiya

Hittiyawa su ne zuriyar Ham ta wurin ɗansa Kan'ana. Sun zama babbar daula da ke a wurin da yau ake kira Turkiyya da kuma arewacin Filistiya.

  • Ibrahim ya kawo ɗan yankin mallaka daga Efron Bahitte domin ya bisne marigayiyar matarsa Sera a cikin kogo a can.
  • Iyayen Isuwa sun damu a lokacin da Isuwa ya auro matan Hittiyawa guda biyu.
  • Ɗaya daga cikin manyan jarumawan Dauda sunansa Yuriya Bahitte.
  • Waɗansu daga cikin bãƙi da Suleman ya auro Hittiyawa ne. Waɗannan bãƙin mata suka karkatar da zuciyar Suleman daga Allah sabo da allohlin ƙarya da suka bautawa
  • Har kusan kullum Hittiyawa sun kasance barazana ga Isra'ilawa, a zahirance da kuma a ruhaniyance.

(Hakanan duba: zuriya, Isuwa, bãƙo, Ham, maɗaukaki, Suleman, Uriya)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • 1 Sarakuna 09:20-21
  • Fitowa 03:7-8
  • Farawa 23:11
  • Farawa 25:10
  • Yoshuwa 01:4-5
  • Nehemiya 09:8
  • Littafin Lissafi 13:27-29