ha_tw/bible/names/hezekiah.md

897 B

Hezekiya

Gaskiya

Hezekiya shi ne sarki na sha uku a cikin sarautar Yahuda. Shi sarki ne da yada dogara da kuma kuma yi wa Allah biyayya.

  • Ba kamar mahaifinsa Ahab ba, wanda ya zama mugun sarki, Hezekiya sarki ne nagari wanda ya rushe dukkan wuraren sujada na gumaka a Yahuda.
  • A wani lokaci ya yi rashin lafiya sosai har ya kusa mutuwa, ya yi addu'a da gaskiya ga Allah domin ya kuɓutar da ransa. Allah ya amsa addu'arsa ya bar shi ya ƙara yin shekaru goma sha biyar.
  • A matsayin alama ta cewa wannan zai faru, Allah ya yi mu'ujjuza na komar da rana baya.
  • Hakanan Allah ya amsa addu'ar Hezekiya ta ceton ransa daga sarki Sennakerib na Asiriya, wanda ke kai masu hari.

(Hakanan duba: Ahaz, Asiriya, allahn ƙarya, Yahuda, Sennakerib)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • 1 Tarihi 03:13-14
  • 2 Sarakuna 16:19-20
  • Hosiya 01:1
  • Matiyu 01:9-11
  • Littafin Misalai 25:1-3