ha_tw/bible/names/habakkuk.md

653 B

Habakuk

Gaskiya

Habakuk annabi ne na Tsohon Alƙawari wanda ya yi rayuwa a wajejen lokacin da Sarki Yehoa'ikim ke mulkin Yahuda. Shima annabi Irmiya yana da rai a dai-dai wanan lokacin.

  • Annabin shi ne ya rubuta littafin Habakuk a wajejen 600 BC a lokacin da Babilawa suka mamaye Yerusalem suka kwashe mutanen Yahuda da yawa zuwa bauta.
  • Yahweh ya ba Habakuk anabci game da yadda "Kaldiyawa" (Babilawa) za su zo su mamaye mutanen Yahuda.
  • Ɗaya daga cikin fittacen jawabin Habakuk shi ne: "Adalin mutum zai rayu ta wurin bangaskiya."

(Hakanan duba: Babila, Yehoa'ikim, Irmiya)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Habakuk 01:2