ha_tw/bible/names/golgotha.md

673 B

Golgota

Gaskiya

"Golgota" sunan wani wuri ne inda aka gicciye Yesu. Sunansa ya zo ne daga kalmar Aremiyanci wadda ke nufin "Wurin Ƙoƙon Kai."

  • Golgota tana bayan garun birnin Yerusalem, can kusa kusa. Tana nan ne gangaren Dutsen Zaitun.
  • A waɗansu tsofaffin fassarori na juyin Littafi Mai Tsarki na turanci, an fassara Golgota da "Kalfari" wadda aka samo daga Latin wadda ke nufin "ƙoƙon kai."
  • Juyi da yawa na Littafi Mai Tsarki na amfani da kalmar da ta yi kama da "Golgota" tun da yake an riga an baiyana kalmar a wurin.

(Hakanan duba: Aram, Tsaunin Zaitun)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Yahaya 19: 17
  • Markus 15:22
  • Matiyu 27:33