ha_tw/bible/names/gideon.md

862 B

Gidiyon

Gaskiya

Gidiyon mutumin Isra'ila ne wanda aka yi renonsa domin ya ceci Isra'ilawa daga maƙiyansu.

  • A wancan lokacin na Gidiyon ke raye, mutanen da ake kira Midiyanawa suna ta kai wa Isra'ilawa hari suna kuma lalatar da amfanin gonakinsu.
  • Ko da yake Gidiyon na jin tsoro Allah ya more shi domin ya jagoranci Isra'ilawa su yi yaƙi gãba da Midiyanawa su kuma yi nasara da su.
  • Gidiyon ya yi biyayya da Allah ta wurin rushe bagadan allohlin ƙarya Ba'al da Ashera.
  • Ba wai jagorancin Isra'ila kawai ya yi ba su yi nasara da maƙiyansu amma har ya ƙarfafa su su yi biyayya da Allah su kuma bauta wa Yahweh, tilon Allah na gaskiya.

(Hakanan duba: Ba'al, Ashera, kuɓutarwa, Midiyan, Yahweh)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Ibraniyawa 11:32-34
  • Littafin Alƙalai 06:11
  • Littafin Alƙalai 06:23
  • Littafin Alƙalai 08: 17