ha_tw/bible/names/gabriel.md

1010 B

Jibira'ilu

Gaskiya

Jibira'ilu sunan ɗaya daga cikin mala'ikun Allah ne. An ambaci sunansa sosai, a cikin Tsohon Alƙawari da kuma Sabon Alƙawari.

  • Allah ya aiko Jibra'ilu ya faɗawa annabi Daniyel ma'anar wahayin da ya gani.
  • Ɗaya lokacin kuma shi ne a sa'ad da Daniyel ke addu'a, mala'ika Jibira'ilu ya hura masa sai ya yi anabci akan abin da zai faru nan gaba. Daniyel ya baiyana shi a matsayin "balagaggen namiji"
  • A cikin Sabon Alƙawari an rubuta cewa Jibira'ilu ya ziyarci Zakariya cewa matarsa Elizabet wadda ta tsufa za ta haifi ɗa, mai suna Yahaya.
  • Watanni shida bayan wanan, aka aiki Jibira'ilu wurin Maryam ya ce da ita Allah zai yi mu'ujuza ta wurin ta za ta yi juna biyu ta haifi ɗa zai kuma zama "Ɗan Allah." Jibira'ilu yace da Maryam ta ba ɗanta suna "Yesu."

(Hakanan duba: mala'ika, Daniyel, Elizabet, Yahaya (mai baftisima) Maryam, annabi, Ɗan Allah, Zakariya)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Daniyel 08:15-17
  • Daniyel 09:21
  • Luka 01:19
  • Luka 01:26