ha_tw/bible/names/david.md

902 B

Dauda

Gaskiya

Dauda shi ne sarki na biyu a Isra'ila ya kuma ƙaunaci Allah. Shi ne babban marubucin littafin Zabura.

  • Tun Dauda na ƙaramin yaro yana kiwon tumakin iyalansu, Allah ya zaɓe shi ya zama sarkin Isra'ila na gaba.
  • Dauda ya zama gwarzon mayaƙi ya kuma jagoranci Isra'ila zuwa yaƙi gãba da maƙiyansu. Ya yi nasara da Goliya hakan kuma sananne ne sosai.
  • Sarki Saul ya so ya kashe shi, amma Allah ya kare shi, ya naɗa shi sarki bayan mutuwar Saul.
  • Dauda ya yi wani zunubi mai ban takaici, amma ya tuba Allah kuma ya gafarta masa.
  • Yesu Masihi, ana kiransa "Ɗan Dauda" domin shi zuriyar sarki Dauda ne.

(Hakanan duba: Goliyat, Filistiyawa, Saul (Tsohon Alƙawari))

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • 1 Sama'ila 17:12 -13
  • 1 Sama'ila 20:34
  • 2 Sama'ila 05: 02
  • 2 Timoti 02:08
  • Ayyukan Manzanni 02: 25
  • Ayyukan Manzanni 13:22
  • Luka 01:32
  • Markus 02:26