ha_tw/bible/names/damascus.md

1.1 KiB

Damaskus

Gaskiya

Damaskus shi ne babban birnin Siriya. Har yanzu yana nan a wurin da yake a cikin kwanakin Littafi mai tsarki.

  • Damaskus na ɗaya daga cikin tsofafufin birane da har yanzu ake zama a cikin duniya
  • A cikin kwanakin Ibrahim, Damaskus ita ce babbar cibiyar masarautar Aram(yanzu tana ƙasar da ake kira Siriya).
  • A cikin dukkan Tsohon Alƙawari, akwai ayoyi da yawa da ke magana kan cunɗanya tsakanin mazaunan Damaskus da mutanen Isra;ila.
  • Ananbce-anabce da yawa na littafi mai tsarki sun yi anabcin hallakarwar Damaskus. Ana tsammanin an cika wannan anabcin a lokacin da Asiriya ta hallakar da birnin a kwanakin tsohon Alƙawari, ko kuma ace akwai tsammanin kammala ƙarasa rushe wannan birni anan gãba.
  • A cikin Sabon Alƙawari Saul Bafarisiye (wanda aka sani da suna Bulus) yana akan hanyarsa domin kamo masubi a birnin Damaskus a lokacin da yesu ya gamu da shi ya kuma sa shi ya zama mai bi.

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • 2 Tarihi 24:23-24
  • Ayyukan Manzanni 09:1-2
  • Ayyukan Manzanni 09: 03
  • Ayyukan Manzanni 26:12
  • Galatiyawa 01:15:-17
  • Farawa 14:15-16