ha_tw/bible/names/colossae.md

977 B

Kolosiya, Kolosiyawa

Gaskiya

A lokacin Sabon Alƙawari, Kolosiya birni ne cikin lardin Roma da ake ce da ita Firijiya, wata gundumar ƙasa ce da yanzu ita ce kudu maso yamma ta ƙasarTurki. Mutanen Kolosiyawa sune mazaunan Kolosiya.

  • Wannan birni misalin mil 100 take daga Tekun Baharmaliya, Kolosiya tana kan muhimmiyar turba ta kasuwanci a tsakanin birnin Afisa da Kogin Ifrates.
  • Sa'ad da Bulus yake a kurkuku a Roma, ya rubuta wa "Kolosiyawa" wasiƙa domin ya gyara wasu koyarwar ƙarya da ke cikin masu bada gaskiya a Kolosiya.
  • Sa'ad da ya rubuta wannan wasiƙa, Bulus bai rigaya ya ziyarci wannan ikilisiya ba, amma ya ji akan waɗanda suka bada gaskiya a nan daga wurin abokin aikin sa, Ifafras.
  • Wataƙila Ifafras shi ne Krista ma'aikaci wanda ya fara kafa ikilisiya a Kolosiya.
  • Littafin Filimon wasiƙa ce ta Bulus zuwa ga ubangidan wani bawa a Kolosiya.

(Hakanan duba: Afisawa, Bulus)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Kolosiyawa 01:03