ha_tw/bible/names/chaldeans.md

800 B

Kaldiya, Ba'kaldiye

Gaskiya

Kaldiya wani yanki ne a kudancin Mesafotamiya ko Babiloniya. Mazaunan wannan yanki ana kiransu Kaldiyawa.

  • Birnin Ur, inda Ibrahim ya fito yana cikin Kaldiya. Yawancin lokaci ana kiransa Ur ta Kaldiyawa."
  • Sarki Nebukanezar ɗaya ne daga cikin Kaldiyawa da yawa da suka yi sarauta akan Babiloniya.
  • Bayan shekaru da yawa, wajen shekarata 600 BC, wannan kalma "Ba'kaldiye" ta zama sananniya da "Babiloniye."
  • A cikin littafin Daniyel, wannan kalma "Ba'kaldiye" ana nufin wasu ƙungiyar mutane ne musamman waɗanda ƙwararrun masana ne da suke bincike taurari.

(Hakanan duba: Ibrahim, Babila, Shina, Ur)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Ayyukan Manzanni 07:4-5
  • Ezekiyel 01:01
  • Farawa 11:27:28
  • Farawa 11:31-32
  • Farawa 15:6-8
  • Ishaya 13:19