ha_tw/bible/names/caesarea.md

1021 B

Siseriya, Siseriya Filifai

Gaskiya

Siseriya birni ne mai mahimmanci a gaɓar Tekun Baharmaliya, kusan kilomita 39 kudu da Tsaunin Karmel. Siserriya Filifai birni ne dake arewa maso gabas da Isra'ila, kusa da Tsaunin Harmon.

  • Waɗannan birane an raɗa masu suna haka saboda Sizozin da suka yi mulkin Roma.
  • Siseriya ta gaɓar teku ta zama cibiyar birni ta lardin Roma na Yahudiya a lokacin da aka haifi Yesu,
  • Manzo Bitrus ya fara wa al'ummai wa'azi a Siseriya ne.
  • Bulus ya tashi daga Siseriya zuwa Tarsus a jirgin ruwa ya kuma wuce ta cikin birnin nan sau biyu a tafiyoyinsa na mai kai bishara.
  • Yesu da almajiransa sun yi tafiya a kewayen lardin nan na Siseriya Filifai cikin Siriya. Dukka biranen biyu an sa masu sunan nan don tunawa da Herod Filib.

(Hakanan duba: siza, al'ummai, teku, Kamel, Tsaunin Hamon, Roma, Tarsus)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Ayyukan Manzanni 09:30
  • Ayyukan Manzanni 10:1-2
  • Ayyukan Manzanni 25:01
  • Ayyukan Manzanni 25:14
  • Markus 08:27
  • Matiyu 16:13-16