1.0 KiB
1.0 KiB
Betel
Gaskiya
- Betel birni ne da yake arewa da Yerusalem a ƙasar Kan'ana. Dã ana ce da shi "Luz."
- Bayan ƙarɓar alƙawarin Allah na farko, Ibram (Ibrahim) ya gina wa Allah bagadi kusa da Betel. Sunan wurin dama ba Betel bane a lokacin, amma aka saba kiransa Betel wanda aka fi sanin sa da shi.
- lokacin da yake guje wa ɗan'uwansa Isuwa, Yakubu ya dakata kusa da birnin nan ya kwanta a ƙasa ya yi barci. Da yake barci, sai ya yi mafarki aka nuna masa mala'iku suna hawa sama suna sauka a bisa wani tsani da ya kai sama.
- Wannan birni ba shi da suna "Betel" sai da Yakubu ya ba shi wannan suna. Domin a gane sosai, wasu masu fassara za su fassara shi su ce "Luz" (daga baya an kira shi Betel) a surorin da aka yi magana akan Ibrahim, da kuma lokacin da Yakubu ya isa can (kafin ya sauya sunan).
- An faɗi Betel sau da yawa a Tsohon Alƙawari kuma wuri ne da muhimman abubuwa suka faru.
(Hakanan duba: Ibrahim, bagadi, Yakubu, Yerusalem)
Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:
- Farawa 12:8-9
- Farawa 35:01
- Hosiya 10:15
- Littafin Alƙalai 01:23