ha_tw/bible/names/abimelech.md

899 B

Abimelek

Gaskiya

Abimelek wani sarkin Filistiyawa ne bisa lardin Gera lokacin da Ibrahim da Ishaku suke zaune cikin ƙasar Kan'ana.

  • Ibrahim ya ruɗi Sarki Abimelek ta wurin cewa Saratu 'yar'uwarsa ce ba matarsa ba.
  • Ibrahim da Abimelek sun yi alƙawari game da mallakar rijiyoyi a Biyasheba.
  • Bayan shekaru da dama, Ishaku ya ruɗi Abimelek da waɗansu mazajen Gera ta wurin cewa Rebeka 'yar'uwarsa ce ba matarsa ba.
  • Sarki Abimelek ya kwaɓi Ibrahim sa'an nan kuma Ishaku domin sun yi masa ƙarya.
  • Wani mutum kuma mai suna Abimelek ɗan Gidiyon ne ɗan u'wan Yotam. Wasu juyin sun canza rubutun sunansa domin su nuna a sarari shi wani mutum ne daban da Sarki Abimelek.

(Hakanan duba: Biyasheba, Gera, Gidiyon, Yotam, Filistiyawa)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • 2 Sama'ila 11:21
  • Farawa 20:03
  • Farawa 20:05
  • Farawa 21:22
  • Farawa 26:11
  • Littafin Alƙalai 09:54