ha_tw/bible/kt/save.md

2.1 KiB

ceto, ceton, cetacce, kãrewa,

Ma'ana

Kalmar "ceta" na nufin kãre wani daga abin da ke na rashin jin daɗi ko na cutarwa. A "kãre" na nufin a shinge daga abin dake cutarwa ko wahala.

  • A mutuntaka, ana kuɓutar da mutane ko a cecesu daga wani abin cuta ko cutarwa ko mutuwa.
  • A ruhaniya, idan aka "ceci" wani, to Allah, ta wurin mutuwar Yesu a kan gicciye, ya gafarta zunubansa ya kuma kuɓutar da shi daga hukuncin lahira domin zunubansa.
  • Mutane na iya ceto ko kuɓutar da mutane daga azaba, amma Allah kaɗai ke iya ceton mutane daga hukunci na har abada domin zunubansu.
  • Kalmar "ceto" na nufin kuɓutarwa daga mugunta da azaba.
  • A cikin Littafi Mai Tsarki, "ceto" na nufin kuɓutarwa ta ruhaniya da azaba ta har abada wadda ke zuwa daga Allah ga waɗanda suka tuba daga zunubansa suka kuma gaskanta da Yesu.
  • Littafi Mai Tsarki kuma ya sake magana game da ceton da Allah ke yiwa mutanensa daga maƙiyansu na zahiri.

Shawarwarin Fassara:

  • Hanyoyin fassara "ceto" sun haɗa da "kuɓuta" ko "kiyayewa daga cutarwa" ko "ɗaukewa daga hanyar cuta" ko "kiyayewa daga mutuwa."
  • Faɗar "dukkan wanda zai ceci ransa," kalmar "ceto" za a kuma iya fassarawa haka "adanawa" ko "kiyayewa."
  • Kalmar "kãrewa" za a iya fassarawa haka "kiyayewa daga haɗari" ko "a wurin da babu abin cutarwa."
  • Kalmar "ceto" za a iya fassarawa da amfani da kalmomin dake dangantaka da "cetowa" ko "cafkowa," a matsayin "Allah ya ceto mutane (daga hukunta su domin zunubansu)" ko "Allah ya cafko mutane (daga maƙiyansu)."
  • "Allah ne cetona" za a iya fassarawa haka "Allah ne wanda ke cetona."
  • "Zaku jawo ruwa daga rijiyoyin ceto" za a iya fassarawa haka "za a wartsakar daku kamar da ruwa saboda Allah yana cafko ku."

(Hakanan duba: gicciye, mai kuɓutarwa, hukunta, zunubi, Mai ceto)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • Farawa 49:18
  • Farawa 47:25-26
  • Zabura 080:08
  • Irmiya 16:19-21
  • Mika 06:3-5
  • Luka 02:30
  • Luka 08:3637
  • Ayyukan Manzanni 04:12
  • Ayyukan Manzanni 28:28
  • Ayyukan Manzanni 02:21
  • Romawa 01:16
  • Romawa 10:10
  • Afisawa 06:17
  • Filibiyawa 01:28
  • 1 Timoti 01:15-17
  • Wahayin Yahaya 19:1-2