ha_tw/bible/kt/pray.md

1.3 KiB

yi addu'a, addu'a, addu'oi, addu'ewa

Ma'ana

Wannan kalma "addu'a" magana ce da Allah. Waɗannan maganganu ana amfani da su kuma ga mutanen da suke ƙoƙarin yin magana da gumaku.

  • Mutane zasu iya yin addu'a shuru, suyi magana da Allah da tunaninsu, ko su yi addu'a da ƙara, suna magana da Allah da muryarsu. Wasu lokatan ana rubuta addu'a, kamar yadda Dauda ya rubuta addu'arsa a Littafin Zabura.
  • Addu'a za ta iya ƙunsar roƙon Allah jinƙai, domin taimako a wata matsala da kuma domin hikima a ɗaukar wasu matakai.
  • Yawancin lokaci mutane sukan roƙi Allah ya warkar da mutane marasa lafiya ko waɗanda suke buƙatar taimakonsa a wasu fannoni.
  • Mutane kuma sukan yi godiya da yabon Allah sa'ad da suke addu'a a gare shi.
  • Addu'a ta haɗa da furta zunubanmu ga Allah da roƙonsa ya gafarta mana.
  • Ana kiran magana da Allah "zumunci" da Allah sa'ad da ruhunmu yana magana da ruhunsa, muna gaya masa yadda muke ji kuma muna jin daɗin kasancewarsa da mu.
  • Za a fassara wannan haka "magana da Allah" ko "zumunta da Allah." Fassara wannan magana yakamata a haɗa har da addu'a shuru.

(Hakanan duba: gunki, gafartawa, yabo)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • 1 Tasalonikawa 03:09
  • Ayyukan Manzanni 08:24
  • Ayyukan Manzanni 14:26
  • Kolosiyawa 04:04
  • Yahaya 17:09
  • Luka 11:1
  • Matiyu 05:43-45
  • Matiyu 14:22-24