ha_tw/bible/kt/peopleofgod.md

1.6 KiB

mutanen Allah, mutanena

Ma'ana

Wannan magana "mutanen Allah" ana nufin mutanen da Allah ya kirawo su daga duniya domin ya kafa wata dangantaka ta masamman da shi kansa.

  • Idan Allah ya ce "mutanena" yana magana ne akan mutanen daya rigaya ya zaɓa kuma suna da dangantaka da shi.
  • Allah ne mai zaɓen mutanensa kuma ya keɓe su daga duniya domin suyi rayuwar da ta gamshe shi. Shi kuma ya kira su 'ya'yansa.
  • A cikin Tsohon Alƙawari, "mutanen Allah" na nufin al'ummar Isra'ila wadda Allah ya zaɓa ya kuma keɓe ta daga sauran wasu al'umman duniya domin su bauta masa su kuma yi masa biyayya.
  • A cikin Sabon Alƙawari "mutanen Allah" masamman ana nufin dukkan waɗanda suka bada gaskiya ga Yesu ana kuma kiran su ikilisiya. Wannan ya haɗa dukka biyu, da Yahudawa da kuma Al'ummai.

Shawarwarin Fassara:

  • Wannan magana "mutanen Allah" za a iya fassara ta a ce "mutane dake na Allah" ko "mutanen dake wa Allah sujada" ko "mutanen dake bauta wa Allah" ko "mutane waɗanda su na Allah ne."
  • Sa'ad da Allah ya ce "mutanena" wasu hanyoyin fassarawa sune "mutanen dana zaɓa" ko "mutanen dake yi mani sujada" ko "mutane waɗanda su nawa ne."
  • Haka kuma "mutanenka" za a iya fassara shi haka, mutanen dake naka" ko mutanen daka zaɓa su zama naka."
  • Kuma "mutanensa" za a iya fasara shi haka "mutanen da su nasa ne" ko "mutanen da Allah ya zaɓa domin su zama nasa."

(Hakanan duba: Isra'ila, ƙungiyar mutane)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • 1Tarihi 11:02
  • Ayyukan Manzanni 07:34
  • Ayyukan Manzanni 07:51-53
  • Ayyukan Manzanni 10:36-38
  • Daniyel 09:24-25
  • Ishaya 02:5-6
  • Irmiya 06:20-22
  • Yowel 03:16-17
  • Mika 06:3-5
  • Wahayin Yahaya 13:7-8