ha_tw/bible/kt/jesus.md

1.8 KiB

Yesu, Yesu Kristi, Kristi Yesu

Ma'ana

Yesu ɗan Allah ne. Sunan "Yesu" na ma'anar "Yahweh na ceto." Kalmar "Almasihu" take ne dake ma'anar "Shafaffe" ana kuma kiran kalmar Kristi ko Mesaya.

  • Yawanci sunayen biyu ana haɗa su a matsayin "Yesu Almasihu, Yesu Kristi" ko "Almasihu Yesu" ko "Kristi Yesu." Wannan na jaddada cewa ɗan Allah shine Mesaya ko Almasihu, wanda ya zo ya ceci mutane daga madawwamin hukuncin azaba domin zunubansu.
  • Ta hanyar al'ajibi, Ruhu Mai tsarki yasa aka haifi madawwamin ɗan Allah aka haife shi a matsayin mutum. Mahaifiyarsa ta wurin mala'ika aka gaya mata cewa ta kira shi "Yesu" domin an ƙaddara shi ya ceci mutane daga zunubansu.
  • Yesu ya aiwatar da al'ajibai da yawa waɗanda suka bayyana cewa shi Allah ne cewa kuma shine Almasihun, ko Mesaya, ko Kristi.

Shawarwarin Fassara:

  • A cikin harsuna da yawa "Yesu" da "Kristi" ana rubuta shi ta hanyar da idan an furta sautin sa zai zama kusan yadda ake furtawa a asalinsa. A misali, "Yesukristo," "Yezus Kristus" "Yesus Kristos," da "Hesukristo" wasu daga cikin hanyoyi ne da ake fassara shi cikin harsuna daban-dabam.
  • Game da taken "Kristi, Almasihu," wasu masu fassarar sunfi so su bar sunan a matsayin "Mesaya" yadda ake rubutawa a harshensu.
  • A kuma yi la'akari da yadda ake rubuta wannan suna a wasu ƙananan harsuna na kusa da manyan harsuna na ƙasa.

(Hakanan duba: Almasihu, Kristi, Allah, Allah Uba, babban firist, masarautar Allah, Maryamu, Mai ceto, Ɗan Allah)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • 1 Korantiyawa 06:11
  • 1 Yahaya 02:02
  • 1 Yahaya 04:15
  • 1 Timoti 01:02
  • 2 Bitrus 01:02
  • 2 Tassalonikawa 02:15
  • 2 Timoti 01:02
  • Ayyukan Manzanni 02:23
  • Ayyukan Manzanni 05:30
  • Ayyukan Manzanni 10:36
  • Ibraniyawa 09:14
  • Ibraniyawa 10:22
  • Luka 24:20
  • Matiyu 01:21
  • Matiyu 04:03
  • Filibiyawa 02:05
  • Filibiyawa 02:10
  • Filibiyawa 04:21-23
  • Wahayin Yahaya 01:06