ha_tw/bible/kt/inherit.md

2.6 KiB

gãdo, abin gãdo, gãdajje, magaji

Ma'ana

Kalmar nan "gãda" na nufin karɓar wani abu mai daraja daga iyaye ko wani mutum sabo da wata dangantaka ta musamman da mutumin nan. "Abin gãdo" shi ne abin da aka gãda ko karɓa.

  • Gãdo na abubuwa shi ne abin da muka karɓa, kamar kuɗi, gona, da dai sauran abubuwa.
  • Gãdo na ruhaniya shi ne duk wani abu da Allah ya ba mutanen da suka yi imani cikin Kristi, waɗanda suka haɗa da albarku na wannan rai da kuma sauran albarku na wannan rai da kuma rai mai zuwa wato rai madawwmi tare da shi.
  • Hakanan Littafi Mai Tsarki ya kira mutanen Allah abin gadonsa, wannan na nufin cewa sun zama mallakarsa mai daraja.
  • Allah ya yiwa Ibrahim alƙawarin cewa zuriyarsa zasu gãji ƙasar Kan'ana da zata zama mallakarsu har abada.
  • Akwai salon magana da ake mora domin ambaton mutanen Allah, wato kamar "magãdan ƙasar" wannan na nuna cewa zasu wadata su zama da albarka ta ruhaniya da kuma ta kayan duniya.
  • A cikin Sabon Alƙawari, Allah ya yi alƙawari cewa waɗanda suka dogara ga Yesu "za su gãjiceto" shima ana kiransa zasu gãji mulkin Allah na har abada.
  • Akwai waɗansu salon magana da ake mora su bada ma'anar waɗannan kalmomin:
  • Littafi Mai Tsarki ya ce mutane masu hikima "za su gãji ɗaukaka" masu adalci kuma za "su gãji managartan abubuwa."
  • Domin "gãdar alƙawaran" wannan na nufin karɓar abubuwa managarta waɗanda Allah ya alƙawarta zai ba mutanensa.
  • Wannan kalma ga marasa azanci ko marasa biyayya za su "gãji wautarsu" wannan na nufin za su gãji ko kuma su karɓi sakamakon ayyukansu na zunubi, wanda ya haɗa da horo sabo da yin rayuwa mara kyau.

Shawarwarin Fassara:

  • Kamar dai yadda da yawa ke yin la'akari cewa ko dai akwai hakikannin wannan kalma a cikin harshen da ake fassara akan wanann kalma magaji, ko gãdo kan iya moron wannan kalmomi.
  • Ya danganta ga wurin, kuma waɗansu hanyoyi da ake fassara wannan kalma "gãdo" za'a iya fassara ta da "karɓa" ko "mallaka" ko "zuwa a mallaka."
  • Da ake yin maganar mutanen Allah akan mãgadansa za'a iya fassara ta da mutanensa masu daraja."
  • Kalmar "magaji" za'a iya fassara ta da dãma ce da ake "mallakar mallakar uba" ko "a sami damar samun gãdar abubuwa na ruhaniya ko albarku."
  • Kalmar nan "abin gãdo" za'a iya fassara ta da "albarku daga wurin Allah" ko kuma "gãdoon albarku."

(Hakanan duba: mãgaji, Kan'ana, Ƙasar Alƙawari)

Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:

  • 1 Korintiyawa 06:9
  • 1 Bitrus 01:04
  • 2 Sama'ila 21:03
  • Ayyukan Manzanni 07:4-5
  • Maimaitawar Shari'a 20:16
  • Galatiyawa 05:21
  • Farawa 15:07
  • Ibraniyawa 09:15
  • Irmiya 02:07
  • Luka 15:11
  • Matiyu 19:29
  • Zabura 079:01