ha_tw/bible/kt/confess.md

30 lines
1.3 KiB
Markdown
Raw Normal View History

2021-06-08 22:05:51 +00:00
# furta, furtawa
## Ma'ana
Furtawa shi ne mutum ya yarda ko ya bayyana cewa wani abu gaskiya ne. "Furtawa" magana ce ko kuma amincewa ne cewa wani abu gaskiya ne.
* Wannan kalma "furta" faɗin gaskiya ne gabagaɗi game da Allah. Zai kuma iya zama bayyana zunubin mu.
* Littafi Mai Tsarki ya ce idan mutane suka furta zunubansu ga Allah, zai gafarta masu.
* Manzo Yakubu ya rubuta a cikin wasiƙarsa cewa idan masu bada gaskiya suka furta zunbansu ga junansu, wannan yana kawo warkaswar ruhaniya.
* Manzo Bulus ya rubuta wa Filibiyawa cewa wata rana kowa zai furta ko yayi shela cewa Yesu Ubangiji ne.
* Bulus kuma ya ce idan mutane suka furta cewa Yesu Ubangiji ne kuma suka gaskata Allah ya tashe shi daga matattu, za su sami ceto.
Shawarwarin Fassara:
* Ya danganta ga yadda ake so a yi amfani da shi cikin rubutu, ga wasu hanyoyin fassara "furtawa" za a iya cewa "yarda" ko "shaidawa" ko "shela" ko "amincewa" ko "tabbatarwa."
* Ga wasu hanyoyi dabam dabam na juya wannan kalma "furtawa" zai iya zama, "furci" ko "shaidawa" ko "magana game da abin da muka gaskata" ko "bayyana zunubi."
(Hakanan duba: bangaskiya, shaida)
Wuraren da ake samunsa a Littafi Mai Tsarki:
* 1 Yahaya 01:8-10
* 2 Yahaya 01:7-8
* Yakubu 05:5-6
* Lebitikos 05:5-6
* Matiyu 03:4-6
* Nehemiya 01:6-7
* Filibiyawa 02:9-11
* Zabura 038:17-18